Search This Blog

Thursday, 19 January 2023

Emeifele Ya Sake Kaiwa Buhari Ziyara A Sirrance

 


Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin  Emefiele, ya shiga bayan labule tare da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a Fadar Gwamnatin Najeriya ta Aso Villa da ke Abuja.

Bayanai sun ce wannan dai ita ce ziyara ta biyu kuma cikin sirri da Gwamnan Babban Bankin Kasar ya kai wa Shugaba Buhari tun bayan dawowarsa Najeriya a ranar 12 ga watan Janairu.

Wannan ziyara na zuwa ne bayan Emefiele ya halarci taron Bankin Bunkasa Tattalin Arziki na Daular Larabawa wanda Darekta Janar na bankin, Dokta Sidi Ould Tah ya jagoranta a ranar Alhamis.

Tun a bara dai labarin Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ya soma yamutsa hazo bayan da aka rika rade-radin cewa jami’an tsaron na sirri na nemansa ruwa a jallo.

A makonnin bayan nan ne dai Emefiele ya bar kasar biyo bayan binciken wasu zarge-zarge da ake yi masa, da suka hada da cin hanci da rashawa da kuma samar da kudade ga ayyukan ta’addanci.

Sai dai tuni CBN ya kore wannan zargi yana mai cewa Emefiele ya ketare kasar nan saboda dalilai na hutun karshen shekara da doka ta ba shi dama.

Gabanin wannan dai, Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta nemi wata Babbar Kotun ta sahale mata cafke Emefiele, amma Alkalin kotun, M.A. Hassan ya yanke hukuncin sanya shamaki tsakanin DSS din da Emefiele.

(AMINIYA)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...