Posts

Showing posts with the label Nijar

Abin Da Ya Kawo Cikas A Sulhun ECOWAS Da Sojin Nijar — Yusuf Tuggar

Image
Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce sun yi tayin tattaunawa domin kawo ƙarshen tankiyar da ke tsakanin Ƙungiyar Raya Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da sojojin da suka kifar da Shugaban Nijar Mohammed Bazoum, amma hakan bai yiwu ba, don kuwa shugabannin sojojin sun ƙi amincewa da yunƙurin. Ambasada Tuggar ya faɗi hakan ne a wata hirarsa da BBC, yana mai cewa duk wata magana da ta shafi a saki Shugaba Bazoum, sojin ba su amince da ita ba. ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 2 a Imo Abdul Amart ya siya wa iyalan Aminu S. Bono gida “Sun ce kar ma a yi wannan maganar, kar ma a sa shi cikin sharuɗɗan yin sulhu,” in ji Yusuf Tuggar. Ya bayyana cewa babu ta yadda za a iya samun sulhu a wannan yanayi. “Za su ci gaba da rike shi kenan ya yi zaman dindindin a kulle?” Ministan ya ce sojojin da suka yi juyin mulki ne suka janyo wa Nijar takunkumin da ECOWAS ta ƙaƙaba mata, da kuma shiga halin da take ciki. Ya ce abin da suke buƙata shi ne a saki Shugaba Bazou

Mun Dakile Yunkurin Bazoum Na Tserewa Daga Nijar Zuwa Najeriya - Sojoji

Image
Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da daƙile wani yunƙurin hamɓararren Shugaban ƙasar Mohamed Bazoum na tserewa tare da iyalinsa. Kakakin gwamnatin sojin Nijar, Kanar-Manjo Amadou Abdramane, wanda ya bayyana hakan cikin jawabin da ya yi wa jama’ar ƙasar ta Talabijin, ya ce Bazoum da iyalinsa sun tsara guduwa daga Fadar Shugaban ƙasar ne da misalin ƙarfe uku na dare. Martanin tubabbun ’yan Boko Haram kan tuban muzuru Kamfanin Nokia zai sallami ma’aikata 14,000 saboda rashin ciniki Ya ce Mohamed Bazoum ya yi kokarin tserewa da karfe 3 na safiyar ranar Alhamis tare da iyalansa masu dafa masu abinci 2 da kuma jami’an tsaro guda biyu. Sai dai a cewar sojojin, wannan yunƙurin da bai kai ga ci ba, na cikin wani tsari da aka shirya da kuma sojojin suka ce suke bi sau da kafa. Kanar-Manjo Amadou Abdramane ya ce “matakin farko na wannan shiri shi ne na su fice daga cikin fadar zuwa kewayen wurin inda wata mota ke jiransu daga nan ne za a dauke su zuwa wani gida da ke cikin unguwar

Labari da dumiduminsa : Kungiyar ECOWAS ta yi la'akari da rikicin soji da 'yan juyin mulkin Nijar, ta bukaci a maido da shugaban kasa.

Image
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta ba da wa'adin kwanaki bakwai ga gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar da ta mayar da shugaban kasar... Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta ba da wa'adin kwanaki bakwai ga gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar da ta maido da shugaba Mohamed Bazoum a matsayin zababben shugaban kasa ta hanyar dimokuradiyya ko kuma ya fuskanci tsauraran takunkumi. Kungiyar ta yankin ta kuma umurci dukkanin hafsan hafsoshin tsaro na kasashe mambobin kungiyar da su ci gaba da gudanar da wani taron gaggawa don tsara dabarun aiwatar da yuwuwar aikin soja na maido da tsarin mulki a ofis. Kungiyar ECOWAS wacce ta amince da Bazoum a matsayin halastaccen shugaban kasar, ta yi barazanar sanya dokar rufe iyakokin kasa da hana zirga-zirgar jiragen sama a jamhuriyar Nijar matukar sojojin da suka kitsa juyin mulkin suka kasa kunnen uwar shegu. Wannan shi ne kudurin babban taron hukumar shugabannin k

Juyin Mulkin Nijar: Ministan Bazoum Ya Nada Kansa Shugaban Gwamnati

Image
Minitsan harkokin wajen Jamhuriyyar Nijar, Hassoumi Massoudou ya ayyana kansa a matsayin Shugaban Gwamnati, yana mai kira ga al’ummar kasar su murkushe juyin mulkin da sojoji suka yi wa Shugaba Mohammed Bazoum. Kawo yanzu dai ba a san hanlin da Mista Bazoum yake ciki ba a hannun masu juyin mulkin. Amma wani sako da aka wallafa ta shafinsa na Twitter a safiyar Alhamis ya ce, “za a kare nasarar da ya samu” kuma al’ummar kasar ne za su tabbatar da hakan. Zargin kashe madugun juyin mulki? Wasu rahotanni daga kasar kuma na cewa sojojin sun kashe wanda ya jagorance su wajen yin juyin mulkin, Abdulrahman Chani. Shugaban gidan rediyon Amfani FM da ke birnin Yamai na kasar, Issoufu Mammane, ya shaida wa Aminiya cewa ana zargin an harbe shi har lahira ne a yayin takaddama kan wanda zai jagoranci gwamnatin sojin, wadda yake neman nada kansa. “A yayin jayayya saboda ya ce shi zai dauki mulki, su kuma sauran sojojin suka ce ba shi zai dauka ba ga wanda za ya dauka (Salifou Modi)… suna wannan