Search This Blog

Showing posts with label Nada sabbin shugabannin Hukumomin Gwamnati. Show all posts
Showing posts with label Nada sabbin shugabannin Hukumomin Gwamnati. Show all posts

Monday, 7 August 2023

Yanzu Yanzu: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Sake Nada Shugabannin Hukumomin Gwamnati

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin karin shugabannin hukumomin gwamnati.

A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, ta ce Wadanda aka nada sune kamar haka.

1. Kabiru Getso Haruna, Babban Sakataren Hukumar ba da tallafin karatu ta Jihar Kano.

2. Farfesa Aliyu Isa Aliyu, Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano.

3. Dr. Kabiru Ado Zakirai, Babban Sakataren Hukumar Kula da Manyan Makarantun Sakandare ta Jihar Kano (KSSMB).

4. Alkasim Hussain Wudil, Coordinator, Cibiyar koyar da sana'o'i Aliko Dangote

5. Farouq Abdu Sumaila, Babban Sakataren Hukumar Ba da Shawara ta Jihar Kano.

6. Alh. Umar Shehu Minjibir, Shugaban Hukumar Ma’aikatan Jihar Kano.

7. CP Kabiru Muhammad Gwarzo mai ritay, Darakta Janar na Cibiyar Tsaro ta Kasuwanci ta Jihar Kano, Gabasawa.

8. Dr. Abdullahi Garba Ali, Darakta, Kano Informatics Institute, Kura.

9. Hajiya Shema'u Aliyu, Darakta a Cibiyar Kula da Baƙi ta Jihar Kano.

10. Dr. Musa Sa'ad Muhammad, Daraktan Cibiyar Wasanni ta Jiha, Karfi.

11. Dr. Abubakar Shehu Minjibir, Daraktan Cibiyar Raya Jarida ta Jihar Kano.

12. Abdullahi S. Abdulkadir, Darakta a Cibiyar sarrafa gonaki ta Jihar Kano, Kadawa.

13. Jazuli Muhammad Bichi, Daraktan Cibiyar Kula Dabbobi ta Jihar Kano, Gargai.

14. Dr. Maigari Indabawa, Daraktan Cibiyar Fina-Finai ta Jihar Kano, Tiga.

15. Kabiru Yusuf, Daraktan Cibiyar Koyar da kiwon  Kifi ta Jihar Kano, Bagauda.

Dukkan nade-naden zai fara aiki nan take kamar yadda aka umurci wadanda aka nada da su karbi sabbin ayyukansu cikin sa'o'i 48 masu zuwa na wannan sanarwar.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...