Posts

Showing posts with the label ilimin yara mata

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar da Gano Illar Bata Tarbiyya Yara Mata A Shirin Tallafawa Ilimi Na AGILE

Image
Biyo bayan zarge-zargen bata tarbiyya da ake yiwa shirin tallafawa ilimin yaya mata na AGILE, ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ta gudanar da taron karawa juna sani na yini biyu kan shirin. Premier Radio ta rawaito a shafinta na Facebook cewa, Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, wanda ya yi magana a yayin taron na masu ruwa da tsakin da ke nazarin horar da dabarun rayuwa a karkashin shirin, ya ce ma’aikatar ta fitar da wani sabon salo na abubuwan da shirin ya kunsa. Ya ce malamai sun yi korafin cewa a cikin shirin akwai wasu abubuwa da basu amince da su ba inda suka duba korafin nasu kuma suka gano matsalar dake cikin sa yayin da aka cire duk wani da ya saba da al’ada da koyarwar addnini muslunci. A nashi bangaren, co’odinetan shirin na AGILE a nan Kano, Alhaji Nasiru Abdullahi-Kwalli, ya ce ma