Posts

Showing posts with the label Abdulmumin Kofa

Abdulmumin Kofa Dispense Money To Constituents For Eid Celebrations

Image
Abdulmumin Jibrin Kofa, the member representing Kiru and Federal Constituency in Kano, continues his longstanding tradition of supporting his constituents by making a generous cash donation for Eid celebrations.  Jibrin handed over the money to the NNPP (New Nigeria Peoples Party) Chairmen of Kiru and Bebeji. He entrusted them with the responsibility of ensuring a fair and equitable distribution, emphasizing the importance of justice and transparency in the process. This year, the donation is set to benefit a wide range of community members, including local leaders, women and youth groups, religious and traditional rulers, as well as social media influencers who play a crucial role in community engagement and information dissemination. The Jarma of Bebeji, who is scheduled to embark on several trips in the coming days, expresses his hope that the donation would bring joy and relief to the beneficiaries during the festive season.  He reiterated his commitment to the welfare

Kofa Ya Raba Tallafin Kudi Ga Mata Guda Dari Biyar A Mazabarsa

Image
A ci gaba da tagomashin arzikin da yake yi wa mutanen mazaÉ“arsa, Abdulmumin Jibrin Kofa, É—an Majalisar Wakilai na Kiru da Bebeji daga jihar Kano, a ranar Lahadi ya sake gwangwaje mata 500 da tallafin kuÉ—i. A sanarwar da h adimin É—an majalisar kan yaÉ—a labarai, Sani Ibrahim Paki  ya fitar, yace an  yi taron rabon tallafin ne a mahaifar É—an majalisar da ke Kofa a Ƙaramar Hukumar Bebeji, Kano, kuma wannan shi ne karo na bakwai da yake raba irin wannan tallafin a ’yan makonnin nan.  Idan za a iya tunawa, a baya É—an majalisar ya raba tallafin ga shugabannin al’umma, mata da matasa, É—alibai, ’yan social media, malamai da masu rike da sarautun gargajiya.  Wannan ne dai rabon tallafi karo na bakwai tun bayan farawa, kuma karo na biyu ga mata. Bugu da Æ™ari, É—an majalisar ya karÉ“i baÆ™uncin fitacciyar ’yar asalin Bebejin nan, kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Hajiya Azumi Babeji, wacce ita ma ta halarci bikin sannan ta gabatar masa da takardar nadin da Gwamnatin Jiha

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Shirya Taron Addu'a Kan Nasarar Kotu, Ya Kuma Tallafa Wa Mutum 10,000

Image
Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Bebeji da Kiru, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya shirya taro na musamman wanda ya haÉ—a sama da mutum 10,000 domin yin addu’o’i a garinsa na Kofa da ke Karamar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano a ranar Lahadi  ÆŠan majalisar mai hawa huÉ—u ya shirya taron ne domin ya gode wa Allah saboda nasarar da ya samu a Kotun Sauraron Ƙararrakin ZaÉ“e da ta ÆŠaukaka Ƙara da ke Abuja a kwanakin baya, da kuma raba wasu kayan tallafi ga ’yan mazabarsa. A yayin kasaitaccen taron dai, an bayar da tallafi ga ’yan mazabar su 10,000 maza da mata. Bugu da Æ™ari, an ba mutanen tallafin kuÉ—i da kayan sanaa da motoci da kayan abinci da sutturu da kuma sauran kayan amfanin yau da kullum. Kazalika, an yi addu’a ta musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin neman Allah Ya ba shi nasara a Kotun ÆŠaukaka Ƙara da ta Ƙoli, da sauran ’yan majalisar Kano na NNPP da suka yi nasara a kotu, da ma fatan nasara ga waÉ—anda ba a kai ga yanke

Kotun Sauraron Zaben 'Yan Majalisar Tarayya Ta Kori Karar Da Aka Shigar Kan Abdulmumin Kofa

Image
Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokokin Jihar Kano da ke zamanta a Kano ta yi Allah-wadai da gazawar Muhammad Said Kiru na jam’iyyar APC wajen gabatar da shedu da dama don tabbatar da cewa ba a yi musu adalci ba a yayin gudanar da zaman Majalisar Wakilai ta Kiru/Bebeji wanda ya yi sanadin rashin samun nasararsa kan karar da ya shigar kan nasarar Abdulmumini. Jibrin Kofa na NNPP Jaridar Justice watch ta rawaito cewa Alkalan kotun uku da ke jagorantar shari’ar mai shari’a Ngozi Flora ta ce takardun da bangarorin biyu suka gabatar a gaban kotun sun nuna Abdulmumini Jibrin Kofa ya yi murabus daga mukaminsa na babban sakataren hukumar gidaje ta tarayya, kwanaki 30 gabanin gudanar da zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu. 2023 a kan ikirarin mai shigar da kara. Mai shigar da kara ya gaza na tabbatar da cewa an tafka kura-kurai a Zabe ba tare da bin dokar zabe ta 2022 kamar yadda aka gyara ba. Don haka an kori karar saboda rashin cancanta. KuÉ—in N100,000 an

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Nada Dr Ahmad Jinjiri Kiru A Matsayin Babban Mataimaka Masa A Harkokin Majalisa

Image
Zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Kiru da Bebeji a jihar Kano  Abdulmumin Jibrin Kofa ya amince da nadin Dr Ahmad Jinjiri Kiru a matsayin babban mai taimaka masa a majalisar tarayya (SLA).  Dr Jinjiri fitaccen dan Kwankwasiyya ne wanda ya amfana da shirin karo karatu da aka yi  Yana da digirin digirgir (PhD) a fannin harkar Akanta tare da gogewar shekaru a fannin Ilimi, jama'a da kuma kamfanoni masu zaman kansu. A wani ci gaban kuma Abdulmumin Jibrin Kofa ya sake nada wasu karin mutum 3 mukamai dadan-daban Wadanda aka nada sun hada da : 1. Ashiru Dankaka Bebeji a matsayin mai taimaka masa kan harkokin majalisa (LA) 2. Bashir Bala Bashir Mai Taimaka masa kan harkokin yada Labarai 3. Umar Ahmad a matsayin Mai daukar hoto.