Search This Blog

Showing posts with label Tinibu. Show all posts
Showing posts with label Tinibu. Show all posts

Monday, 21 August 2023

Cancanta Muka Duba Wajen Zaɓo Ministoci — Tinubu

Shugaban Bola Ahmed Tinubu ya ce cancanta ce ta yi tasiri wajen zaɓo ministocinsa da aka rantsar a yau domin su taimaka wajen tafiyar da lamurran ƙasar.

Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da ya yi jawabi bayan rantsar da sabbin ministoci a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

“Ƴan Najeriya na sa ran za ku yi aiki mai inganci kuma za ku sauke nauyin da aka ɗora muku,” in ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa “Dole ne ku yi aikin da zai sanya ƴan Najeriya su sake amincewa da gwamnati.”


Ya bayyana cewa akwai babban nauyi a kan sabbin ministoci ganin irin manyan alƙawurran da gwamnatinsa ta ɗauka.

Shugaban ya kuma buƙaci sabbin ministocin da su yi aiki ba tare da nuna banbanci ba, inda ya ce: ”An ba ku wannan matsayi ne ba domin ɓangaren da kuka fito ku jihonhinku ba, sai dai domin ƙasa baki ɗaya.”
(AMINIYA)

Friday, 4 August 2023

Tsakanin Maryam Shetty Da Mariya Mahmoud: Yadda abokiyar Karatu Ta Maye Gurbin Abokiyar Karatunta A Kunshin Ministocin Tinibu

Shugaba Bola Tinubu ne ya nada Maryam Shettima wanda aka fi sani da Maryam Shetty minista, amma Mariya Mahmoud abokiyar karatunta na kan hanyarta na rantsar da sabuwar ministar aka sanar da ita cewa an cire sunanta

Tinubu ya sanya sunan Shetty a cikin kashi na biyu na ministocin da aka aika wa majalisar dattawa ranar Laraba.


Sai dai duk da haka, an yi ta cece-kuce da suka da suka da suka biyo bayan nadin da aka soke ranar Juma’a.

Mutane da yawa sun yi kuskure a zabin Shetty wanda ke da dimbin magoya baya a shafukan sada zumunta. Wasu sun siffanta ta a matsayin Tik Toker kawai.

Tinubu ya ajiye Maryam Shetty, ya zabi Keyamo, Mahmud a matsayin ministoci

An yi ta sukar wanda aka nada a matsayin minista a wani sakon Twitter inda ya tunkari Tinubu

Amma yayin da Shetty ta isa majalisar dokokin kasar domin tantancewa a ranar Juma’a, an cire sunan ta.

ad
An maye gurbinta da Mahmoud abokin karatunta daga JSS 1 zuwa JSS 3 a Makarantar Sakandare na Gidauniyar Kano, sannan kuma a Jami'ar Bayero ta Kano.

Matan guda biyu sun rabu a  sashen Kimiyyar Kiwon Lafiyar Kiwon Lafiya kuma sun ɗauki wasu kwasa-kwasan tare. Shetty ta karanta Physiotherapy yayin da Mahmoud ya karanta Likita da tiyata.

Mahmoud tana daya daga cikin kwamishinonin makusantan na farko a lokacin Ganduje.

Ita kuma kawa ce ga Amina Ganduje, daya daga cikin jiga-jigan 'ya'yan shugaban jam'iyyar APC na kasa a yanzu.

Ita ma Amina Ganduje Likita ce wadda ta kammala karatun digiri a Jami’ar Maiduguri kuma ta yi aiki da Mahmoud a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH).


Akwai jita-jita cewa Amina ta nada kwamishinoni biyu ko fiye a majalisar ministocin mahaifinta, inda ake hasashen Mahmoud daya ne.

(Daily Trust)

Monday, 29 May 2023

Za a ci gaba da amfani da tsofaffin kudi —Tinubu

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa za a ci gaba da amfani da tsoffin kudin da gwamnatin Buhari ta soke.

Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar sauyin kudi da gwamnatin Buhari ta yi.
Tinubu wanda ya bayyana hakan bayan an rantsar da shi, ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar haraji, domin saukaka wa ’yan kasuwa gudanar da harkokinsu domin samun sauki da nufin bunkasa bangaren.

Tinubu ya soke biyan tallafin mai
Shugaban Kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur.

Tinubu ya ce tallafin mai ya zama tarihi ne jim kadan bayan an ranstar da shi a Dandalin Eagle Square da ke Abuja.

Ya ce biyan tallafin abu ne ba mai dorewa ba, don haka gara a yi amfani da kudaden da ake kashewa wajen biyan tallafin domin yin wasu ayyukan raya kasa.

AMINIYA 

Wednesday, 17 May 2023

Labari da dumiduminsa : Tinibu Zai Zo Kano Domin Bude Ayyuka - Ganduje

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa ana sa ran zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai zo jihar kano domin bude wasu aiyuka da gwamnatinsa gudanar a nan kano.

 
” A yayin da muka cigaba da bude wasu daga cikin aiyukan raya kasa da gwamnatinmu ta yi a kwarya birnin kano da kewaye, Muna sa rana Zaɓaɓɓen Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da sabuwar gadar da muka Samar a kofar mata zuwa Ibrahim Taiwo Road”.


Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar ta jihar kano na wannan makon a gidan gwamnatin jihar kano.


Ganduje yace ya bude aiyuka Masu tarin yawa Kuma zai cigaba da bude aiyukan don raya kasa da gwamnatinsa ta gudanar.

Ganduje dai ya na bude aiyukan da ya gudanar ne a wani bangare na bankwana ga al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa a ranar 29 ga watan mayu.

Tuesday, 16 May 2023

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje


Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa.

Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa.

Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023.
Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu.

Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar.

A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai mai barin gado, Femi Gbajabiamila, ne suka raka shi.

Majiyar ta ce “Matar Tinubu, Sanata Oluremi ce ta karbi bakuncin Hajiya Hafsa, a yayin da ‘yan siyasar kuma suka dauki tsawon lokaci suna tattauna a kan hadin kan kasa da abubuwan da sabuwar gwamnati za ta ba wa muhimmanci.

“Sauran sun hada da batun shugabancin Majalisar Dokoki ta Kasa da kuma aniyar zababben shugaban kasan na kafa gwamnatin hadin kan kasa da ake fatan damawa da Kwankwaso a ciki.

“Sun kuma yi waiwaye a kan kawancensu na siyasa tun suna lokacin da suke Majalisar Dokoki ta Kasa a shekarar 19992,” in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa a yayin zaman an kuma fara tunanin sasanta tsakanin Kwankwaso da tsohon mataimakinsa, wato Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A shekarar 2015 Ganduje ya gaji kujerar Kwankwaso, amma ba da jima ba daga baya suka raba gari, kuma har yanzu ba sa ga-maciji.
AMINIYA 

Da dumi-dumi: Kwankwaso yayi ganawar sa’o’i hudu da Tinubu a birnin Paris

Zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, sun yi ganawar akalla sa’o’i hudu a birnin Paris na kasar Faransa a ranar Litinin, kamar yadda jaridar TheCable ta ruwaito.

A tsakiyar tattaunawar, TheCable ta fahimci cewa, akwai yuwuwar shigar Kwankwaso cikin gwamnati mai zuwa yayin da Tinubu ke shirin kafa “gwamnatin hadin kan kasa” – wanda ke nufin bai wa jam’iyyun adawa wasu mukamai a cikin gwamnatin.


Taron ya kuma tattauna batutuwan da suka shafi zaben shugabannin majalisar kasa, gabanin kaddamar da majalisar ta 10 a ranar 13 ga watan Yuni.

Zaben gwamnan kano: Inda aka Kwana game da karar APC da NNPP a Kotu

An fara taron Paris tsakanin Tinubu da Kwankwaso ne da karfe 12:30 na rana kuma aka kammala da karfe 4:45 na yamma, kamar yadda wasu majiyoyi suka shaida wa jaridar TheCable.

Ko Kun zabi aiki ko ba ku zaba ba, mun yi titin Kurna babban layi ne saboda Allah -Ganduje

Femi Gbajabiamila, kakakin majalisar wakilai kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, ya halarci taron yayin da Abdulmumin Jibrin, dan takarar jam’iyyar NNPP kuma tsohon jigo a kwamitin yakin neman zaben Tinubu na daga cikin wadanda suka raka Kwankwaso.

Oluremi Tinubu, Sanata kuma matar zababben shugaban kasa ita ce ta tarbi matar Kwankwaso, Salamatu.

Idan za’a iya tunawa Tinubu da Kwankwaso sun yi aiki a matsayin gwamnonin kano da Lagos a Shekarar 1992.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...