Posts

Showing posts with the label Tinibu

Cancanta Muka Duba Wajen Zaɓo Ministoci — Tinubu

Image
Shugaban Bola Ahmed Tinubu ya ce cancanta ce ta yi tasiri wajen zaɓo ministocinsa da aka rantsar a yau domin su taimaka wajen tafiyar da lamurran ƙasar. Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da ya yi jawabi bayan rantsar da sabbin ministoci a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja. “Ƴan Najeriya na sa ran za ku yi aiki mai inganci kuma za ku sauke nauyin da aka ɗora muku,” in ji Tinubu. Ya ƙara da cewa “Dole ne ku yi aikin da zai sanya ƴan Najeriya su sake amincewa da gwamnati.” Ya bayyana cewa akwai babban nauyi a kan sabbin ministoci ganin irin manyan alƙawurran da gwamnatinsa ta ɗauka. Shugaban ya kuma buƙaci sabbin ministocin da su yi aiki ba tare da nuna banbanci ba, inda ya ce: ”An ba ku wannan matsayi ne ba domin ɓangaren da kuka fito ku jihonhinku ba, sai dai domin ƙasa baki ɗaya.” (AMINIYA)

Tsakanin Maryam Shetty Da Mariya Mahmoud: Yadda abokiyar Karatu Ta Maye Gurbin Abokiyar Karatunta A Kunshin Ministocin Tinibu

Image
Shugaba Bola Tinubu ne ya nada Maryam Shettima wanda aka fi sani da Maryam Shetty minista, amma Mariya Mahmoud abokiyar karatunta na kan hanyarta na rantsar da sabuwar ministar aka sanar da ita cewa an cire sunanta Tinubu ya sanya sunan Shetty a cikin kashi na biyu na ministocin da aka aika wa majalisar dattawa ranar Laraba. Sai dai duk da haka, an yi ta cece-kuce da suka da suka da suka biyo bayan nadin da aka soke ranar Juma’a. Mutane da yawa sun yi kuskure a zabin Shetty wanda ke da dimbin magoya baya a shafukan sada zumunta. Wasu sun siffanta ta a matsayin Tik Toker kawai. Tinubu ya ajiye Maryam Shetty, ya zabi Keyamo, Mahmud a matsayin ministoci An yi ta sukar wanda aka nada a matsayin minista a wani sakon Twitter inda ya tunkari Tinubu Amma yayin da Shetty ta isa majalisar dokokin kasar domin tantancewa a ranar Juma’a, an cire sunan ta. ad An maye gurbinta da Mahmoud abokin karatunta daga JSS 1 zuwa JSS 3 a Makarantar Sakandare na Gidauniyar Kano, sannan kuma a Jami&#

Za a ci gaba da amfani da tsofaffin kudi —Tinubu

Image
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa za a ci gaba da amfani da tsoffin kudin da gwamnatin Buhari ta soke. Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar sauyin kudi da gwamnatin Buhari ta yi. Tinubu wanda ya bayyana hakan bayan an rantsar da shi, ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar haraji, domin saukaka wa ’yan kasuwa gudanar da harkokinsu domin samun sauki da nufin bunkasa bangaren. Tinubu ya soke biyan tallafin mai Shugaban Kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur. Tinubu ya ce tallafin mai ya zama tarihi ne jim kadan bayan an ranstar da shi a Dandalin Eagle Square da ke Abuja. Ya ce biyan tallafin abu ne ba mai dorewa ba, don haka gara a yi amfani da kudaden da ake kashewa wajen biyan tallafin domin yin wasu ayyukan raya kasa. AMINIYA 

Labari da dumiduminsa : Tinibu Zai Zo Kano Domin Bude Ayyuka - Ganduje

Image
Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa ana sa ran zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai zo jihar kano domin bude wasu aiyuka da gwamnatinsa gudanar a nan kano.   ” A yayin da muka cigaba da bude wasu daga cikin aiyukan raya kasa da gwamnatinmu ta yi a kwarya birnin kano da kewaye, Muna sa rana Zaɓaɓɓen Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da sabuwar gadar da muka Samar a kofar mata zuwa Ibrahim Taiwo Road”. Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar ta jihar kano na wannan makon a gidan gwamnatin jihar kano. Ganduje yace ya bude aiyuka Masu tarin yawa Kuma zai cigaba da bude aiyukan don raya kasa da gwamnatinsa ta gudanar. Ganduje dai ya na bude aiyukan da ya gudanar ne a wani bangare na bankwana ga al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa a ranar 29 ga watan mayu.

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje

Image
Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa. Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje. A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa. Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023. Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu. Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar. A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin

Da dumi-dumi: Kwankwaso yayi ganawar sa’o’i hudu da Tinubu a birnin Paris

Image
Zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, sun yi ganawar akalla sa’o’i hudu a birnin Paris na kasar Faransa a ranar Litinin, kamar yadda jaridar TheCable ta ruwaito. A tsakiyar tattaunawar, TheCable ta fahimci cewa, akwai yuwuwar shigar Kwankwaso cikin gwamnati mai zuwa yayin da Tinubu ke shirin kafa “gwamnatin hadin kan kasa” – wanda ke nufin bai wa jam’iyyun adawa wasu mukamai a cikin gwamnatin. Taron ya kuma tattauna batutuwan da suka shafi zaben shugabannin majalisar kasa, gabanin kaddamar da majalisar ta 10 a ranar 13 ga watan Yuni. Zaben gwamnan kano: Inda aka Kwana game da karar APC da NNPP a Kotu An fara taron Paris tsakanin Tinubu da Kwankwaso ne da karfe 12:30 na rana kuma aka kammala da karfe 4:45 na yamma, kamar yadda wasu majiyoyi suka shaida wa jaridar TheCable. Ko Kun zabi aiki ko ba ku zaba ba, mun yi titin Kurna babban layi ne saboda All