Posts

Showing posts with the label Dokar Ta Baci

Gwamnatin Kano Ta Sanya Dokar Ta Baci A Kan Fannin Ilimi

Image
Daga Nasiru Yusuf Ibrahim  Gwamnatin jihar Kano za ta kafa dokar ta-baci a fannin ilimi.  Kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana haka a ranar Litinin a wajen taron karawa juna sani na kwanaki uku domin bunkasa shirin ilimi na bangaren na shekara wanda aka gudanar a Kaduna.  Kwamishinan ya ci gaba da cewa a ranar 6 ga watan Mayun wannan shekara ne gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf zai ayyana dokar ta baci a fannin ilimi.  Doguwa ya ce da wannan sanarwar da aka yi niyya, ilimi zai jagoranci gaba, a matsayin abin da gwamnati ta sa a gaba.  Kwamishinan ya bayyana cewa nan da makwanni biyu jihar za ta kaddamar da shirin shigar da dalibai, a masarautun biyar inda za su bayar da shawarwari da sarakuna, gundumomi, kauye da masu unguwanni domin inganta karatun dalibai a makarantun firamare.  Doguwa ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta amince da bukatu da dama da ma’aikatar ilimi ta gabatar. Don haka kwamishinan ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba gwam