Posts

Showing posts with the label shaidar cin zabe

Zababben Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf na ya al'ummar Kano domin su Karbar Shaidar Cin Zabensa

Image
Zababben Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida Gida yana gayyatar dumbin magoya bayansa, mambobin jam'iyyar NNPP da kuma manyan masu ruwa da tsaki, zuwa gabatar da takardar shaidar cin zabe ga dukkan 'yan takarar da suka ci zabe a ranar Asabar 18 ga wata. Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Kano ta shirya ranar Laraba 29 ga Maris, 2023 da karfe 10 na safe a sakatariyar INEC don bayar da shaidar cin zabe ga zababben gwamna da mataimakinsa da ‘yan majalisar jiha. Kakakin zababben gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, a wata sanarwa a ranar Talata ya ce za a gudanar da taron ne a dakin taro na INEC da karfe 10:00 na safe. Ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar NNPP da duk wadanda aka gayyata, wadanda suka shahara da son zaman lafiya da bin doka da oda, da su rika gudanar da harkokinsu cikin tsari a lokacin bikin da kuma bayan bikin, tare da yi wa kowa fatan alheri. SABATURE