Posts

Showing posts with the label Zagon Kasa

Ba Ma Yi Wa Shirin Mika Mulki Zagon Kasa - Ganduje

Image
Gwamnatin jihar Kano  ta ce a shirye take domin miƙa mulki ga sabuwar gwamnati cikin ruwan sanyi ba tare da tayar da ƙura ba. Cikin wata sanarwa da ta fitar mai ɗauke da sa hannun kwamishinan yaɗa labarai Muhammad Garba, gwamnatin ta ce tuni aka samar da babban kwamiti da kuma ƙanana da za su taimaka domin ganin an miƙa mulkin salin alin. Ya musanta iƙirarin jam’iyyar NNPP da ta ke jiran karɓar mulki na cewa gwamnatin Ganduje na yi wa shirin miƙa mulki zagon ƙasa. Kwamishinan ya ƙara da cewa kwamitin miƙa mulki na ɓangaren gwamnatin Ganduje na rubuta rahoton ƙarshe kafin miƙa mulki. Ya bayyana cewa kamata ya yi kwamitin karɓa na gwamnati mai jiran gado shi ma ya shirya domin karɓar rahoton, wanda ya yi alƙawarin miƙawa a kan lokaci. Muhammad Garba ya ƙara da cewa manufar miƙa mulki shi ne gwamnati mai sauka ta miƙa duk wasu abubuwa na tafiyar da shugabanci cikin ruwan sanyi. Ba yunkurin yaɗa wani tunani ko wata aƙida ba. Ya kuma ce kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta ma

Bayan Zargin Yi Wa Takararsa Zagon Kasa, Tinubu Ya Ziyarci Buhari A Daura

Image
  Yan kwanaki bayan ya zargi Gwamnatin Tarayya da kokarin yi wa takararsa kafar ungulu, ta hanyar wasu manufofinta, dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya ziyarci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a mahaifarsa da ke Daura a Jihar Katsina. Tinubu dai ya sami rakiyar Gwamnan Jihar ta Katsina, Aminu Bello Masari da wasu Gwamnonin APC, yayin ziyarar da daren Juma’a, kamar yadda wasu majiyoyi suka tabbatar wa Aminiya. Sai dai babu cikakkun bayanai kan ainihin makasudin ziyarar ta Tinubu zuwa Daura. A ranar Alhamis ce Aminiya ta rawaito yadda Tinubu ya yi zargin gwamnati mai ci ta kirkiro matsalar wahalar man fetur da canjin kudin da suka jefa ’yan Najeriya cikin kunci a ’yan kwanakin nan da gangan ne domin ta gurgunta takararsa. Lamarin dai ya yi ta yamutsa hazo a fagen siyasar Najeriya, inda wasu suke zargin akwai alamun baraka tsakanin dan takarar da gwamnatin jam’iyyarsa. Amma Kakakin Kwamitin Yakin Neman Zaben Tinubu, Byo Onanuga, ya zargi ’yan adawa da kokarin rura wu