Posts

Showing posts with the label Zabe

Labari Da Dumiduminsa: Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kano Ta Sanar Da Ranar Zaben Kananan Hukumomi

Image
Shugaban Hukumar, Farfesa Sani Lawan Malumfashi, shi ne ya sanar da hakan a safiyar ranar Laraba, yayin da yake yi wa manema labarai bayani  Malumfashi ya kara da cewa Hukumar za ta gudanar da zaben ne a ranar 30 ga Watan Nuwanba na 2024 Yayi amfani da taron wajen yin Kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki, su tallafawa Hukumar don gudanar da sahihin zabe Cikakken Labarin zai zo muku nan gaba 

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Enugu, Kano, Akwa Ibom Sakamakon Rikici, Sace Jami'an Zabe

Image
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta dakatar da sake gudanar da zabukan da aka gudanar a wasu mazabu na jihohin Enugu, Kano, da Akwa Ibom, sakamakon tarzoma, da rashin bin ka’ida, da kuma sace jami’an zabe. Yankunan da abin ya shafa sun hada da mazabar Enugu ta Kudu 1 a jihar Enugu, da kuma mazabar tarayya ta Ikono/Ini a jihar Akwa Ibom, da kuma mazabar Kunchi/Tsanyawa dake jihar Kano. Wannan sanarwar ta fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sam Olumekun, kwamishinan na kasa & shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu zabe, a ranar Asabar. Dakatarwar ta biyo bayan rahotannin ‘yan daba da sace kayan zabe a wadannan jihohin. A mazabar Enugu ta Kudu 1, an dakatar da zabukan a dukkan runfunan zabe takwas da aka yi na farko A mazabar Kunchi da Tsanyawa da ke jihar Kano, an dakatar da zabuka a dukkanin mazabu goma da ke karamar hukumar Kunchi sakamakon mamayewa da barna da kuma kawo cikas da ‘yan daba. An yanke wannan hukuncin ne bisa ga sashe

Yau INEC Za Ta Taron Gaggawa Kan Zaben Adamawa

Image
A yau Talata Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) za ta gudanar ta taron gaggawa da ta kira kan dambarwar sakamakon zaben gwamnan Jihar Adamawa da ya tayar da kura. Daga taron ne za a ji shawarar da INEC ta yanke a game da sakamakon zaben gwamnan, wanda a ranar Lahadi hukumar ta dakatar da tattarawa saboda rikicin da ya dabaibaye shi. A ranar Litinin hukumar ta dakatar da Kwamishinan Zabe (REC) na Jihar Adamawa, Barista Hudu Yunus Ari, saboda ya yi gaban kansa wajen ayyana Sanata Aisha Dahiru Binani ta Jam’iyyar APC a matsayin zababbiyar gwamna, alhali ba a kammala tattara sakamakon zaben ba. Lamarin dai ya yamutsa hazo, amma Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, wanda yake neman a zaben a Jam’iyyar PDP, ya bukaci jama’a su kwantar da hankalinsu, domin INEC za ta dauki matakin da ya dace. Tuni dai Fintiri da PDP da kungiyoyin kare dimokuradiyya suka yi tir da abin da kwamishinan zaben ya yi, inda suka bukaci INEC ta dauki mataki a kan wannan kwamacala. Rikicin zaben ya dauki sabon

Za Mu Kama Duk Wanda Ya Dauki Makami Ranar Zabe A Kano —’Yan Sanda

Image
  Mataimakin babban sufeto-Janar na ’yan sanda DIG Hafiz Muhammad Inuwa da ke kula da harkokin zaben shekarar 2023 a yankin jahohin Arewa maso Yammacin Najeriya, ya gargadi ’yan siyasa da magoya bayansu, da su kauce wa yin wani abu da zai tada hankulan masu zabe.  DIG Hafiz M. Inuwa ya bayyana cewa shugaban ’yan sanda Usman Alkali Baba ya umarce su, da su gargadi ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki da su ja wa magoya bayansu kunne gabanin zaben da ke tafe a ranar Asabar 18 ga watan Maris 2023. Ya bayyana hakan ne a Jihar Kano, a ci gaba da shirye-shirye da rundunar ke yi na tabbatar da tsaro da kare rayukan al’umma da kuma dukiyoyinsu. Ya kara da cewa fatansu, shi ne a yi zabe lafiya a kammala lafiya, ba tare da nuna siyasa da gaba ba. “Duk wani dan siyasa in dai yana son ci gaban Kano, to zaman lafiya shi ne ci gaban, so ake a zauna lafiya. “Kuma na zo da jawabi, in gargade su, Wallahi ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen maganin duk wani da ya nemi ya tada fitina, “Saboda haka ina tabbata

INEC Ta Gargadi Masu Sanya Idanu Kan Zaben Najeriya

Image
Hukumar Zaɓen Najeriya, INEC, ta gargaɗi masu aikin sa ido kan yadda zaɓukan ƙasar za su gudana su kiyaye da dokoki da ƙa'idojin ƙasar sannan su guji katsa-landan a abin da ba su da hurumi a kai. INEC ta yi gargaɗin ne a lokacin da ta gudanar da taron ƙarin haske game da dokokin aikin sa idon da bayar da bayanai ga masu aikin na cikin gida da kuma na waje a Abuja, ranar Talatar nan. Tuni dubban masu sa idon suka hallara a ƙasar domin duba yadda zaɓukan - da za a fara ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu - za su gudana, inda za a fara da na shugaban ƙasa da na 'yan majalisun dokoki na tarayya. Sai kuma ranar 11 ga watan Maris inda za a yi zaɓukan gwamnoni da 'yan majalisun dokoki na jihohi Dubban masu sanya idanu daga ƙungoyoyi daban-daban na ciki da wajen Najeriya ne suka saurari bayanai daga manyan jami'ai na hukumar zaɓen da suka haɗa da shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu da sauran muƙarraban hukumar game da yadda kowa zai taka rawar da ta dace b

Sabbin Katinan Zabe 13m Muka Buga —INEC

Image
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) na bincike kan zargin jami’anta da karbar na goro a aikin rabon katin zabe da ke gudana. Hukumar ta kara da cewa ta buga sabbin katinan zabe miliyan 13 da dubu 868 da 441 bayan kammala aikin rajistar sabbin masu zabe. Da yake sanar da hakan, Kwamishinan INEC na Kasa kan Wayar da Masu Zabe da Yada Labarai, Festus Okoye, ya ce, “Hukumar ta damu bayan samun korafe-korafe kan nuna fifiko a wasu wuraren rabon katin. “Duk halastattun masu rajista na da ’yancin karbar katinsu domin kada kuri’a a ranar zabe a wuraren da suka yi rajista.” Ya ci gaba da cewa, “Don haka wajibi ne Kwamishinonin Zabe su tabbatar babu nuna wariya a rabon katin, tare da hukunta jami’ai masu kunnen  kashi. “Domin kawar da shakku, sabbin katunan zabe miliyan 3 da dubu 868 da 441 INEC ta buga da suka hada da na sabbin wadanda suka yi rajista da wadanda suka sauya wurin zabe da kuma wadanda aka sabunta katinsu.” Okoye ya sanar cewa hukumar ta kara lokacin rabon katin zuwa ranar 29 ga watan Jan

Kamawa zasu maimaita abun da ya faru a zaben 1993 - Ganduje

Image
Abdullahi Umar Ganduje, ya ce Kanawa za su sake maimaita abin da ya faru a zaben Shugaban Kasa na 1993, inda suka goyi bayan dan takarar da ya fito daga yankin Kudu – suka yi watsi da nasu na Arewa kuma dan asalin jihar. Ganduje ya yi wannan furuci ne a yayin wani rangadin yakin neman zabe da ya fita tare da ’yan takarar jam’iyyar APC masu neman mukamai daban-daban a zabe mai zuwa. Aminiya ta ruwaito cewa gwamnan ya yi furucin ne yayin da ya ziyarci Hakimin Kibiya, Sunusi Abubakar Ila, bayan gudanar da taron yakin neman zabe da tuntubar juna a kananan hukumomin Rano da Bunkure na jihar. A zahiri dai Ganduje ya tabbatar da goyon bayansa ga dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, inda ya yi hannun riga da tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda ke takarar kujerar Shugaban Kasa a jam’iyyar NNPP. A jawabinsa yayin hikaito tarihi, Ganduje ya ce, “Mun zabi Cif MKO Abiola na jam’iyyar SDP kuma muka ki amincewa da Bashir Othman Tofa na jam’

Akwai Yiwuwar Matsalar Tsaro Ta Kawo Wa Zaben 2023 Tangarda – INEC

Image
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa matsalar tsaron da ake fama da ita a wasu sassan Najeriya za ta iya sa wa a soke babban zaben 2023 da za a fara a watan gobe. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, wanda Shugaban Cibiyar Bincike Kan Harkokin Zabe (BEI), Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta ne ya yi gargadin ranar Litinin a Abuja. Ya bayyana hakan ne yayin wani taron ba da horo kan shirye-shiryen tsaro a lokacin zaben. Hukumar ta ce matsalar na iya sa wa a gaza gudanar da zaben a mazabu da dama, ta yadda zai yi wahala a iya bayyana wanda ya lashe shi, wanda ta ce hakan zai haifar da rudani a tsarin mulkin Najeriya.

Mutanen Kano sun tabbatar min da yakinin zan lashe zabe - Tinubu

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewar yana da yakinin jam’iyyar za ta kai ga nasara duba da irin fitowar dangon-kwari da magoya suka yi mata a Jihar Kano. Jaridar Aminiya ta rawaito cewa A ranar Talata ce dai Tinubu ya ziyarci Kano don kaddamar da yakin neman zabensa a Arewa Maso Yamma, gabanin shiga zaben Shugaban Kasa a wata mai kamawa. Da yake jawabi ranar Laraba a filin wasa na Sani Abacha, Tinubu ya ce, “Manuniya ta nuna cewa a yakin neman zaben nan, jama’ar Kano sun san abin da ya kamata su zaba. “Ina da yakinin goyon bayan da Gawuna da Garo ke samu zai kai jam’iyyar nan ga nasarar lashe zaben gwamna har zuwa na Shugaban Kasa,” in ji Tinubu. Tinubu ya bayyana farin cikinsa kan yadda mutane suka yi dafifi don nuna goyon bayansu ga takararsa. A nasa bangaren, Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bukaci magoya baya da su kada wa jam’iyyar APC kuri’arsu a babban zaben da ke tafe. Ganduje ya bai wa Tinubu tabbacin

Obasanjo ba zai iya kawo mazabarsa ba - Tinubu

Image
Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya gargadi Peter Obi, cewa kada ya rudu da goyon bayansa da tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ke yi. Tinubu ya ce goyon bayan Obasanjo ba zai kai Peter Obi ko’ina ba, saboda Obasanjo ba zai iya lashe akwatin mazabarsa ba. “Bincikenmu mun gano Obasanjo bai taba nasarar sa wani ya lashe kujerar shugaban kasar Najeriya ba. “Ko a Jihar Ogun babu wanda zai dogara da shi don lashe kujerar gwamna ko kansila,” in ji Tinubu  ta hnnun Daraktan yada labarai na kwamitin yakin neman zaben Tibubu, Bayo Onanuga. Ya ci gaba da cewa, “Muna tausaya wa Peter Obi domin Obasanjo ba zai iya lashe masa akwatin mazabarsa da ke Abeokuta ba a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.” Tsohon gwamnan na Legas, ya bayyana yadda Obasanjo ya goyi bayan tsohon mataimakinsa, Atiku Abubakar a zaben 2019 kuma ya sha kaye a hannun Shugaba Buhari. Tinubu ya jadadda cewa da taimakonsa Buhari ya samu gagarumar nasara a zaben tare da ti