Posts

Showing posts with the label 2023

Ranar Malamai Ta Duniya 2023: Gwamna Abba Kabir Ya Jinjinawa Malaman Kano

Image
A yayin da al’ummar duniya ke bikin ranar malamai ta duniya 2023 a yau wadda Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin gudanar da bikin ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga malaman jihar da su jajirce wajen ganin sun kammala aikinsu. A sanarwar da babban sakataren Yada labaran gwamnan, Sunusi Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, Gwamna Abba Kabir Yusuf a lokacin da yake tsokaci kan kokarin malamai na tunawa da ranar malamai ta duniya ta bana, Gwamnan ya bayyana su a matsayin masu gina kasa wanda dole ne kowace gwamnati mai kishin kasa ta ba su kulawa sosai. Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za a iya karawa da irin gudunmawar da malamai suke bayarwa ba domin su ne mataki na ginshikin horar da ma’aikatan da suke daukaka a kowane fanni na ayyukan dan Adam. Alh Abba Kabir ya jaddada shirye-shiryen gwamnatin sa na inganta koyo da koyarwa ta hanyar gaggauta biyan albashi, karin girma, horaswa, sake horarwa da sa

Bayan Ficewa Daga Tafiyar Tinubu, Naja’atu Ta Koma Wajen Atiku

Image
  Fitacciyar ’yar siyasar nan ta Jihar Kano kuma daya daga cikin tsofaffin Daraktocin kamfen din dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, Naja’atu Muhammad, ta koma wajen dan takarar PDP, Atiku Abubakar. Matakin nata na zuwa ne ’yan sa’o’i bayan ta sanar da ajiye mukamin na Tinubu, tare da ayyana ficewarta daga jam’iyyar mai mulki. Ta tabbatar da hakan ne yayin ziyarar da ta kai wa Atiku a gidansa ranar Lahadi. Daga bisani dai ta shaida wa  Aminiya  cewa yanzu tana goyon bayan takarar ta Atiku a zabe mai zuwa. A baya dai, Naja’atu, wacce ita ce Daraktar Kungiyoyin Fararen Hula a Kwamitin Yakin Neman Zaben Tinubu, ta ce za ta gana da ’yan takarar jam’iyyun siyasa kafin ta dauki matsaya kan wanda za ta mara wa baya. Ta ce ta dawo daga rakiyar Tinubu ne saboda a cewarta, sam ba ya iya yin tunani da kansa. Ta ce, “Gaskiya ne yanzu ba na yin Tinubu, dalili ke nan ma da na bar jam’iyyar. Abubuwa da dama sun faru, da kyar yake iya tunani da kwakwalwarsa. Wannan ko shakka babu,

Akwai Yiwuwar Matsalar Tsaro Ta Kawo Wa Zaben 2023 Tangarda – INEC

Image
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa matsalar tsaron da ake fama da ita a wasu sassan Najeriya za ta iya sa wa a soke babban zaben 2023 da za a fara a watan gobe. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, wanda Shugaban Cibiyar Bincike Kan Harkokin Zabe (BEI), Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta ne ya yi gargadin ranar Litinin a Abuja. Ya bayyana hakan ne yayin wani taron ba da horo kan shirye-shiryen tsaro a lokacin zaben. Hukumar ta ce matsalar na iya sa wa a gaza gudanar da zaben a mazabu da dama, ta yadda zai yi wahala a iya bayyana wanda ya lashe shi, wanda ta ce hakan zai haifar da rudani a tsarin mulkin Najeriya.

2023: Peter Obi Ne Dan Takarata —Obansajo

Image
  A karon farko tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya fito bainar jama’a ya bayyana goyon bayansa ga dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP, Peter Obi, a zaben 2023. Da yake bayyana goyo bayan nasa a cikin sakonsa na murnar shiga Sabuwar Shekarar 2023, Obasanjo ya ce Peter Obi ya yi wa sauran ’yan takarar shugaban kasa fintinkau wajen  ilimi da kwarewa. https://noordakata.blogspot.com/2023/01/abdulmumin-jibrin-kofa-ya-raba-tallafin.html https://noordakata.blogspot.com/2023/01/gwamnan-jihar-kano-abdullahi-umar.html A cikin sakonsa nasa mai mai taken, “Rokona ga ’yan Najeriya, musamman matasa,” Obasanjo ya ce, “Duk da cewa a cikin masu masu takarar babu wani shafaffe da mai, amma a cikin Peter Obi ya fi sauran nagarta ta bangaren kyawun dabi’u, gogewa, fahimta, abin da suka yi a baya da wanda za su iya kawowa.” “Sauran kuma, kamar kowannenmu na da irin gudunmawar da zai bayar a sabuwar gwamantin wajen farfado da al’amura da kuma ceto Najeriya. “Dadin dadawa, Peter Obi allura da

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace 'yan arewa basu da wanda zasu zaba sama da Bola Tinubu

Image
  Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce ’yan Arewa ba su da wani dalili ko kadan da zai hana su zabar dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu. Ya ce dan takarar tasu ya yi sadaukarwa mai tarin yawa wajen bunkasa Dimokuradiyya a Najeriya, musamman wajen kokarinsa na cicciba dan Arewa ya zama Shugaban Kasa. Saboda haka, Ganduje ya ce yanzu ne daidai lokacin da ya dace a rama wa kura aniyarta. . https://noordakata.blogspot.com/2022/12/sojojin-haya-sun-kama-jirgi-maare-da.html . https://noordakata.blogspot.com/2022/12/gasar-sukuwar-dawaki-ta-premier-ta.html Ganduje ya bayyana haka ne yayin wani taro da wata kungiya mai suna Volunteers for Democracy, karkashin Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Usman Alhaji ta shirya a Kano ranar Asabar. A cewar Gwamnan, “Babu wani hanzari da ’yan Arewa suke da shi na kin zabar APC da dan takararta, Bola Tinubu. “A baya, ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarar ’yan Arewa, don haka ya kamata mu ma mu nuna halacci. “Tinubu ya g