Search This Blog

Showing posts with label 2023. Show all posts
Showing posts with label 2023. Show all posts

Thursday, 5 October 2023

Ranar Malamai Ta Duniya 2023: Gwamna Abba Kabir Ya Jinjinawa Malaman Kano

A yayin da al’ummar duniya ke bikin ranar malamai ta duniya 2023 a yau wadda Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin gudanar da bikin ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga malaman jihar da su jajirce wajen ganin sun kammala aikinsu.


A sanarwar da babban sakataren Yada labaran gwamnan, Sunusi Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, Gwamna Abba Kabir Yusuf a lokacin da yake tsokaci kan kokarin malamai na tunawa da ranar malamai ta duniya ta bana, Gwamnan ya bayyana su a matsayin masu gina kasa wanda dole ne kowace gwamnati mai kishin kasa ta ba su kulawa sosai.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za a iya karawa da irin gudunmawar da malamai suke bayarwa ba domin su ne mataki na ginshikin horar da ma’aikatan da suke daukaka a kowane fanni na ayyukan dan Adam.

Alh Abba Kabir ya jaddada shirye-shiryen gwamnatin sa na inganta koyo da koyarwa ta hanyar gaggauta biyan albashi, karin girma, horaswa, sake horarwa da sauran ayyukan ci gaban malamai (TDPs) don koyar da inganci da inganci a makarantu.

Ya kara da cewa, ta hanyar kwamitin sake wayar da kan al’umma (CRC), gwamnati za ta gyara ajujuwa da bandakuna da wuraren ruwa a makarantun.

"Za mu karfafa tare da dorewar shirye-shiryen ciyar da makarantun firamare domin kara yawan zuwa da kuma rage illar rashin abinci mai gina jiki a Kano, ko shakka babu hakan zai inganta yanayin koyo da koyarwa a makarantunmu."

A cewar Gwamnan, domin ganin an samar da aikin ba da ilimi kyauta, an tanadi raba riguna guda biyu ga daliban makarantun firamare domin tabbatar da cewa duk yaron da ya kai makaranta ya shiga makaranta ba tare da la’akari da matsayin iyayensa na zamantakewa da tattalin arziki ba.

Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga malaman jihar da su kara kaimi tare da yin iyakacin kokarinsu domin cimma burin daukaka jihar nan ta fuskar ci gaban ilimi.



Monday, 23 January 2023

Bayan Ficewa Daga Tafiyar Tinubu, Naja’atu Ta Koma Wajen Atiku

 


Fitacciyar ’yar siyasar nan ta Jihar Kano kuma daya daga cikin tsofaffin Daraktocin kamfen din dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, Naja’atu Muhammad, ta koma wajen dan takarar PDP, Atiku Abubakar.

Matakin nata na zuwa ne ’yan sa’o’i bayan ta sanar da ajiye mukamin na Tinubu, tare da ayyana ficewarta daga jam’iyyar mai mulki.

Ta tabbatar da hakan ne yayin ziyarar da ta kai wa Atiku a gidansa ranar Lahadi.

Daga bisani dai ta shaida wa Aminiya cewa yanzu tana goyon bayan takarar ta Atiku a zabe mai zuwa.

A baya dai, Naja’atu, wacce ita ce Daraktar Kungiyoyin Fararen Hula a Kwamitin Yakin Neman Zaben Tinubu, ta ce za ta gana da ’yan takarar jam’iyyun siyasa kafin ta dauki matsaya kan wanda za ta mara wa baya.

Ta ce ta dawo daga rakiyar Tinubu ne saboda a cewarta, sam ba ya iya yin tunani da kansa.

Ta ce, “Gaskiya ne yanzu ba na yin Tinubu, dalili ke nan ma da na bar jam’iyyar. Abubuwa da dama sun faru, da kyar yake iya tunani da kwakwalwarsa. Wannan ko shakka babu, mai musu kuma ya je ya nemi bidiyonsa ya kalla.

“Ni ba na la’akari da bambancin addini ko kabilanci a siyasa, shi ya sa tunanina ya fadada. Lokaci ya yi da ya kamata mu ajiye son zuciya mu ciyar da kasarmu gaba. Ba zai yiwu mu ci gaba da tafiya a haka ba. Dalilina ke nan, amma ba ni da wata nifaka a kan kowa,” in ji ta.

Monday, 9 January 2023

Akwai Yiwuwar Matsalar Tsaro Ta Kawo Wa Zaben 2023 Tangarda – INEC



Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa matsalar tsaron da ake fama da ita a wasu sassan Najeriya za ta iya sa wa a soke babban zaben 2023 da za a fara a watan gobe.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, wanda Shugaban Cibiyar Bincike Kan



Harkokin Zabe (BEI), Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta ne ya yi gargadin ranar Litinin a Abuja.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron ba da horo kan shirye-shiryen tsaro a lokacin zaben.

Hukumar ta ce matsalar na iya sa wa a gaza gudanar da zaben a mazabu da dama, ta yadda zai yi wahala a iya bayyana wanda ya lashe shi, wanda ta ce hakan zai haifar da rudani a tsarin mulkin Najeriya.

Sunday, 1 January 2023

2023: Peter Obi Ne Dan Takarata —Obansajo

 


A karon farko tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya fito bainar jama’a ya bayyana goyon bayansa ga dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP, Peter Obi, a zaben 2023.

Da yake bayyana goyo bayan nasa a cikin sakonsa na murnar shiga Sabuwar Shekarar 2023, Obasanjo ya ce Peter Obi ya yi wa sauran ’yan takarar shugaban kasa fintinkau wajen  ilimi da kwarewa.

  • https://noordakata.blogspot.com/2023/01/abdulmumin-jibrin-kofa-ya-raba-tallafin.html
  • https://noordakata.blogspot.com/2023/01/gwamnan-jihar-kano-abdullahi-umar.html

A cikin sakonsa nasa mai mai taken, “Rokona ga ’yan Najeriya, musamman matasa,” Obasanjo ya ce, “Duk da cewa a cikin masu masu takarar babu wani shafaffe da mai, amma a cikin Peter Obi ya fi sauran nagarta ta bangaren kyawun dabi’u, gogewa, fahimta, abin da suka yi a baya da wanda za su iya kawowa.”

“Sauran kuma, kamar kowannenmu na da irin gudunmawar da zai bayar a sabuwar gwamantin wajen farfado da al’amura da kuma ceto Najeriya.

“Sannan yana da mataimaki wanda matsashi ne mara tabo a bangaren nasarorin da ya samu a rauyuwa, da kuma harkokin jama’a,” in ji sakon na Obasanjo.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace 'yan arewa basu da wanda zasu zaba sama da Bola Tinubu

 



Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce ’yan Arewa ba su da wani dalili ko kadan da zai hana su zabar dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu.

Ya ce dan takarar tasu ya yi sadaukarwa mai tarin yawa wajen bunkasa Dimokuradiyya a Najeriya, musamman wajen kokarinsa na cicciba dan Arewa ya zama Shugaban Kasa.

Saboda haka, Ganduje ya ce yanzu ne daidai lokacin da ya dace a rama wa kura aniyarta.

. https://noordakata.blogspot.com/2022/12/sojojin-haya-sun-kama-jirgi-maare-da.html

. https://noordakata.blogspot.com/2022/12/gasar-sukuwar-dawaki-ta-premier-ta.html

Ganduje ya bayyana haka ne yayin wani taro da wata kungiya mai suna Volunteers for Democracy, karkashin Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Usman Alhaji ta shirya a Kano ranar Asabar.

“A baya, ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarar ’yan Arewa, don haka ya kamata mu ma mu nuna halacci.

“Tinubu ya goyi bayan Buhari a gwagwarmayarsa har ya zama Shugaban Kasa. Bai nemi a biya shi da kowanne irin matsayi ba a gwamnati, kuma ya ci gaba da goyon bayan gwamnatin.

“Ni ban ma taba ganin masoyin ’yan Arewa ba kamar shi,” inji Ganduje

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...