Search This Blog

Wednesday, 4 January 2023

Gwamnatin tarayya za ta dena biyan tallafin man Fetur

 


Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce daga ƙarshen watan Yunin wannan shekara za ta daina biyan tallafin man fetur a ƙasar.

Ministar kuɗi, kasafi da tsare-tsare ta ƙasar Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a lokacin gabatar da kasasfin kuɗin shekarar 2023.

BBC Hausa ta rawaito cewa Misis Zainab ta ce gwamnatin tarayya ta ware kimanin naira tiriliyan 3.36 domin biyan tallafin man fetur ɗin a cikin wata shida na farkon shekarar 2023.

Ministar ta ƙara da cewa hakan na daga cikin tsarin tsawaita cire tallafin zuwa wata 18 da gwamnatin ta bayyana a shekarar da ta gabata.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...