Posts

Showing posts with the label Almundahana

Hukumar Karbar Korafe Korafe Ta Kano Ta Kama Tsohon Kwamishinan Ganduje Da Wasu Sauran Mutane Bisa Zargin Yin Almundahana Da Kudi Sama Da Naira Biliyan Daya

Image
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta kama tare da tsare kwamishinan ayyuka da samar da ababen inganta rayuwa na tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, Injiniya Idris Wada Saleh da wasu mutane biyar bisa zargin almundahanar Naira biliyan 1. SOLACEBASE  ta tattaro cewa an kama kwamishinan wanda kuma shi ne Manajan Darakta na Hukumar Kula da gyara titinan Kano da Babban Sakatare na Hukumar Kula da Kayayyakin Jama’a, Mustapha Madaki Huguma, Daraktan Kudi, Daraktan Bincike da Tsare-tsare tare da wasu a ranar Litinin da yamma bisa zargin karkatar da sama da Naira biliyan gyaran hanyoyi 30 da magudanar ruwa a cikin babban birni da ba a yi ba. Wata majiya a hukumar ta shaida wa SOLACEBASE  cewa an biya kudaden da aka cire a Kaso uku a cikin asusun kamfanoni uku a ranar 25 ga Afrilu, 2023. “Abin mamaki har hukumar kula da harkokin gwamnati ta bayar da satifiket na rashin kin amincewa da kwangilar bayan an biya kudin kwanaki goma da suka gabata wanda ya sabawa dokar sayan

Almundahanar N96bn: Wike Ya Sake Maka Amaechi A Kotu

Image
Gwamnatin Ribas ta shigar da sabuwar kara kan tsohon gwamnan jihar kuma tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, kan zargin yin sama da fadi da Naira biliyan 96. An maka Amaechi tare da Tonye Cole, dan takarar gwamna na Jam’iyyar APC a jihar bisa zargin sayar da kadarorin jihar. HOTUNA: Masaukin Ronaldo da burwarsa a Saudiyya DAGA LARABA: Dalilin Da Maza Ke Tsoron Auren Mata ’Yan Boko  Zacchaeus Adangor, babban lauyan Gwamnatin Jihar Ribas, ya tabbatar da shigar da karar. Nyesom Wike, gwamnan Ribas, ya kafa wani kwamitin mutum bakwai don bincikar Amaechi kan zargin cirar Naira biliyan 96 daga asusun gwamnatin jihar a lokacin da yake gwamna. Kwamitin ya kuma binciki batutuwan da suka shafi sayar da kadarorin da tsohon gwamnan ya yi. Kwamitin ya gabatar da rahotonsa a 2015 kan binciken, amma Amaechi ya musanta aikata laifin da ake tuhumar sa. A ranar 27 ga Mayu, 2022, wata babbar kotu ta yi watsi da bukatar Amaechi na hana kwamitin gudanar da bincike a kansa. Sakamakon haka ne