Posts

Showing posts with the label Kamfanin jirgin Arik

Nan Ba Da Jimawa Ba Kamfanin Jirgin Arik Zai Kammala Jigilar Alhazai 'Yan Jirgin Yawo - NAHCON

Image
Kamfanin jirgin sama na Arik Zai Kammala Aikin Jigilar Alhazai Na jirgin Yawo Nan Ba ​​da jimawa ba A cewar sanarwar da mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar, Fatima Sanda Usara, bayanin da ya iske hukumar alhazan Najeriya NAHCON daga bangaren masu gudanar jigilar jirgin yawo musamman ma daga bangaren Legas, na bukatar a nuna damuwa. Hukumar ba ta da masaniya a kan lamarin, kuma a baya ta yi amfani da duk abin da ta ke da shi don shawo kan lamarin kafin ya zama ya ta'azzara.  NAHCON na gab da kulla sabuwar yarjejeniya da za ta baiwa dukkan maniyyatan kamfanoni masu zaman kansu da suka biya domin jigilar su ta jirgin Arik Air zuwa kasar Saudiyya lafiya kamar yadda aka tsara. Hakika NAHCON ta kulla yarjejeniya da Arik Air na jigilar maniyyata kusan 7,000 da suka yi rajista da hukumomin balaguro masu zaman kansu na aikin Hajjin 2023.  A nasa bangaren, Arik ya sanya hannu kan yarjejeniyar da wani kamfanin jiragen sama na kasar Saudiyya don jigilar kasons