Posts

Showing posts with the label Kudin Fansa

Dokar Najeriya Ta Haramta Biyan Kuɗin Fansa — Ministan Tsaro

Image
  Ministan Tsaro Mohammed Badaru Abubakar ya ce Dokar Najeriya ta haramta biyan masu garkuwa da mutane kuɗin fansa. Ministan wanda ya bayyana haka ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a wannan Larabar, ya ce lokaci ya yi da za a daina biyan kuɗin fansar saboda haka ne kaɗai hanyar kawo ƙarshen masu garkuwa da mutane. Ya ce Shugaban Kasa ya bai wa dukkan hafsoshin tsaro goyon bayan da ya kamata don ganin an kawo karshen garkuwa da mutane da ya yi ƙamari a ƙasar. Tsohon Gwamnan na Jihar Jigawa, ya ce kasancewar dokar Najeriya ta haramta bayar da kuɗin fansa ya sanya bai kamata mutane su riƙa biyan kuɗin ba saboda ba shi da amfani. “Babbar matsalar ita ce yadda mutane ke fitowa a kafafen yaɗa labarai suna neman taimako, har a zo a tara musu kuɗi domin biyan fansa. Hakan bai dace ba. “Idan muka daina biyan kuɗin fansa, sannu a hankali ayyukan masu garkuwa da mutane zai zama tarihi,” in ji Badaru. Dangane da yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a Abuja, babban birnin ƙasar da kuma g

Dogo Gide Na Neman N100m Kan Daliban FGC Birnin Yauri

Image
Iyayen daliban da aka sace a Sakandaren Gwamnatin Tarayya (FGC) ta Birnin Yauri a Jihar Kebbi na neman agaji, bayan dan ta’addan da ya sace su, Dogo Gide, ya sa musu kudin fansa Naira miliyan 100. Dogo Gide ya sanya sharadin biyan Naira miliyan 100 ne duk da iyayen yaran sun bi ta hannun mahaifiyarsa ta matsa masa lamba ya sako ragowar ’yan mata 11 da ke hannusa kusan tsawon shekara biyu. Maharan jirgin Edo na neman fansar N520m NAJERIYA A YAU: Ma’aikatar Shari’a ta fadi gwajin tsare gaskiya —ICPC “Mun yi magana da Dogon Gide ranar 15 ga wagan Disamba, 2022, da farko ya ki magana, amma bayan mahaifiyarsa ta sa baki, ya amince zai sako yaranmu idan mun biya Naira miliyan 1oo, ko kuma mu hakura da su. “Ya fada karara cewa idan ba mu yi abin da ya ce ba, har abada ba za mu sake jin duriyar ’ya’yanmu ba,” in ji Shugaban kungiyar iyayen daliban, Salim Kaoje. Ya bayyana haka ne a wani taro da suka yi a makarantar a ranar Lahadi, inda suka ce sun riga sun ga gazawar gwamnati wajen