Posts

Showing posts with the label Kwazo

Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, Shi Ne Ministan Da Ya fi Kowanne Nuna Kwazo A Najeriya - Triangle News Media

Image
A ranar 6 ga Mayu, 2023, a birnin Landan na kasar Birtaniya, Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki, Farfesa Isa Ali Ibrahim (Pantami) FCIIS, FBCS, FNCS, ya samu lambar yabo ta "Fitaccen Minista" ta Mujallar Triangle.  A sanarwar da mataimaki na musamman ga Ministan kan kafafen sadarwa na zamani, Yusuf Abubakar ya wallafa, an bayar da wannan lambar yabon ne saboda kwazo, aiki tukuru, kyakkyawan jagoranci da kuma kwazon aiki da Farfesa Pantami ya nuna, wanda ke neman sanya bangaren tattalin arzikin na Najeriya a kan turbar ci gaba. A karkashin jagorancin Farfesa Pantami, fannin tattalin arziki na dijital ya sami nasarorin da ba a taÉ“a gani ba a fannonin shiga yanar gizo, fasahar dijital da kasuwanci, haÉ—a dijital, ka'idojin ci gaba, kariyar bayanai da sirri, da Æ™warewar dijital, da sauransu. Minista Pantami da kan sa ya jajirce wajen samar da wasu muhimman kudirori guda biyu na bangaren tattalin arzikin Najeriya, wato Nigeria Startup Act 2022, dokar da

Malamai Da Tsofaffin Soji Ba Sa Kwazo A Jagoranci —Obasanjo

Image
Tsohon Shugaban Kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya ce galibi ba a samun wani ci gaba na a zo a gani a jihohin da suka kasance karkashin jagorancin malamai ko tsofaffin soji. Obasanjo ya ce babu wani ci gaban da aka samu a jihohin kasar nan da ke karkashin jagorancin mutane masu rike da matsayin Farfesa ko Dakta da tsoffin sojoji, har ma da malaman makarantu. Tsohon Shugaban na Najeriya na wannan furuci a jawabinsa yayin wani taro kan zurfafa al’adun dimokuradiyya da aka gudanar ranar Alhamis a Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas. Obasanjo ya ce duk da yake an samu wasu jajirtattun shugabannin da ba su da yawa, akasarinsu ba sa iya mulki mai kyau saboda rashin samun mataimaka na gari, abin da ke hana su jagorancin da ake bukata. A cewarsa, rashin tattaunawa tsakanin shugabannin da masu taimaka musu, kan haifar da gibi wajen musayar ra’ayi, matakin da ke hana samun fahimtar juna da hadin-kai wajen cimma manufar ci gaba da ake bukata. Obasanjo ya ce, bayan kwashe shekaru 60 da sa