Posts

Showing posts with the label Gargadi

Mataimakin Gwamnan Kano Ya Umarci Shugabannin Kwamitin Riko Da Su Ci Gaba Da Zama A Kananan Hukumominsu

Image
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya umurci shugabannin kwamitocin riko na kananan hukumomi 44 da su zauna ko su koma kananan hukumomin da aka nadasu. Gwarzo ya bayar da umarnin ne a jiya (Asabar) yayin da yake karbar sama da mutane 1000 da suka sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa New Nigerian Peoples Party (NNPP) daga Shanono a gidan gwamnati dake Kano. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu ya raba wa manema labarai a ranar Lahadi. Mataimakin Gwamna Gwarzo, wanda kuma yake rike da mukamin kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, ya jaddada mahimmancin shugabannin kwamitocin riko su kasance cikin shiri a kananan hukumomin da aka nadasu. Ya umarce su da su tafi zuwa majalisunsun kananan hukumominsu tare da fara ayyuka masu tasiri a sassa masu mahimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, da samar da ruwa. Mataimakin gwamnan ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da shugaban

Ba Zamu Lamunci Yi Mana Katsalandan A Ayyukanmu Ba - EFCC

Image
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta yi kira ga jama’a  cewa laifi ne a hana jami’an hukumar gudanar da ayyukansu na halal. A sanarwar da Shugaban sashen hulda da jama'a na hukumar,  Dele Oyewale  ya sanyawa hannu, yace Sashi na 38(2)(a(b) na dokar kafa hukumar EFCC ya sanya laifin hana jami'an hukumar gudanar da ayyukansu na halal. Masu laifi suna fuskantar daurin kurkuku na kasa da shekaru biyar. Wannan gargadin ya zama dole bisa ga yadda mutane da kungiyoyin da Hukumar ke bincike ke kara ta'azzara na daukar doka a hannunsu ta hanyar daukar 'yan baranda domin dakile ayyukan EFCC. A lokuta da dama, jami’an Hukumar sun yi taka-tsan-tsan wajen tunkarar irin wannan tada zaune tsaye domin gujewa tabarbarewar doka da oda. Abin takaici, ana É—aukar irin wannan halin a matsayin alamar rauni. Don haka hukumar ta yi gargadin cewa daga yanzu ba za ta lamunci duk wani yunkurin wani mutum ko kungiya na kawo cikas ga ayyukanta ba domin kuw

NAHCON Ta Gargadi Jama'a Kan Yada Labaran Karya Na Daukar Aiki

Image
Wannan sanarwa ce daga hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) na fadakar da alhazai musulmi masu niyyar zuwa aikin Hajji, da masu neman aikin likita ko duk wani mai sha’awa game da yadda ake yada sakonnin bogi dangane da daukar aiki a tawagar likitocin NAHCON.   A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin yada labarai da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace labari ya riski hukumar cewa ana yada bayanan karya ga daidaikun mutane da ke ikirarin daukar ma’aikata na dundundun a NAHCON ko a matsayin mambobin tawagar likitoci da sauran mambobin kwamitin aikin Hajji. A halin yanzu NAHCON ba ta daukar ma’aikata na dundundun , ko wasu ma’aikata a kan haka da duk wani sakon da ke nuni da cewa karya ne.   Sahihan tsarin aikace-aikacen tawagar likitocin Hajji ana gudanar da shi ne ta hanyar shafin hukumar na yanar gizo kuma har yanzu tana ci gaba. Hukumar ta bukaci jama’a da su yi watsi da duk wata hanyar sadarwa ta daban, su dogara ne kawai da bayanai daga tashar

Hukumar NAHCON Ta Gargadi Hukumomin Alhazai Na Jihohi Kan Fadar Kudin Kujerar Da Ya Zarta Wanda Ta Ayyana

Image
Tuni dai hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta bayyana cewa, ana ta tafka ta’azzara ce a bayan da hukumar ta sanar da fara biyan kudin hajjin karshe na shekarar 2023 a daidai lokacin da wasu jihohi ke bayyana farashin da ya sha bamban da wanda aka amince .  Jihohi da Hukumar sun amince da kuma yadda Gwamnati ta amince. Don haka, muna gaggawar sake maimaita abubuwa kamar haka: Da farko dai jimillar kudin Hajji ya kasance wanda Hukumar ta sanar a ranar Juma’a 7 ga Afrilu, 2023 wanda bai kai Naira miliyan uku (N3,000,000) da ya hada da kudin gida na dukkan nau’in Alhazai da ke karkashin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha. A cewar sanarwar da mataimakin daraktan yada labarai na hukumar NAHCON, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu,  ta ce Yana da kyau a yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da cewa mu yi aiki tare cikin jituwa da kwanciyar hankali da lumana, ta yadda za mu guji duk wani mataki na cin gajiyar Alhazai. Ta kara da cewa duk da yake ba mu damu da halin kuÉ—aÉ—en wasu Jihohi ba,

INEC Ta Gargadi Masu Sanya Idanu Kan Zaben Najeriya

Image
Hukumar Zaɓen Najeriya, INEC, ta gargaɗi masu aikin sa ido kan yadda zaɓukan ƙasar za su gudana su kiyaye da dokoki da ƙa'idojin ƙasar sannan su guji katsa-landan a abin da ba su da hurumi a kai. INEC ta yi gargaɗin ne a lokacin da ta gudanar da taron ƙarin haske game da dokokin aikin sa idon da bayar da bayanai ga masu aikin na cikin gida da kuma na waje a Abuja, ranar Talatar nan. Tuni dubban masu sa idon suka hallara a ƙasar domin duba yadda zaɓukan - da za a fara ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu - za su gudana, inda za a fara da na shugaban ƙasa da na 'yan majalisun dokoki na tarayya. Sai kuma ranar 11 ga watan Maris inda za a yi zaɓukan gwamnoni da 'yan majalisun dokoki na jihohi Dubban masu sanya idanu daga ƙungoyoyi daban-daban na ciki da wajen Najeriya ne suka saurari bayanai daga manyan jami'ai na hukumar zaɓen da suka haɗa da shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu da sauran muƙarraban hukumar game da yadda kowa zai taka rawar da ta dace b