Posts

Showing posts with the label Masu Mukamai

Shugaban Kungiyar NOSPA ya Bukaci Wadanda Tinubu Ya Nada Mukami Su Mika Kansu Ga Shugabancin Jami'iyyar

Image
Shugaban Kungiyar masu goyon bayan jam’iyyar APC ta North-South Progressive Alliance (NOSPA), Alwan Hassan, ya yi kira ga duk wadanda aka nada a gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da su nuna cikakken biyayyarsu tare mika kansu ga tsarin jam’iyyar APC , wanda a karkashinsa aka kafa gwamnati. Hassan ya yi wannan kiran ne a wata ziyara daban-daban da ya kai wa jakadan Najeriya a kasar Jamus Ambasada Yusuf Tuggar da tsohon gwamnan jihar Kano Alh. Abdullahi Ganduje. A cewarsa, saboda kasancewarsu ‘ya’yan jam’iyyar APC, kasancewarsu jam’iyyar da ke kan gaba wajen tafiyar da harkokin mulki, shugaban kasa Bola Tinubu ya ba su damar yi wa kasarsu hidima kuma bai kamata a yi amfani da wannan dama ta hanyar rashin biyayya da kuma nuna adawa da su BA dokokin jam'iyyar. “Wajibi ne wadanda aka nada su kasance a cikin zuciyarsu cewa an yi kira da su taimaka wa shugaban kasa wajen cika alkawuran da aka yi wa ‘yan Najeriya a cikin Manifesto na jam’iyyar APC, don haka dole ne su m