Posts

Showing posts with the label Sojoji

An ceto mutane 386 bayan shekaru 10 a hannun Boko Haram

Image
Sojoji sun ceto fararen hula 386, akasarinsu mata da kakanan yara, daga Dajin Sambisa, bayan Boko Haram ta sace su kimanin shekaru goma da suka gabata. Mai rikon mukamin Babban Kwamandan Birget Din Sojin Kasa Na 7, Birgedia AGL Haruna, ne ya bayyana haka ranar Lahadin yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen dajin da ke karamar hukumar Konduga ta jihar Borno sakamakon nasarar kammala wani aiki na kwanaki 10 da aka yi wa lakabi da “Operation Desert Sanity 111”. A cewarsa, an kai farmakin ne da nufin kawar da duk wani burbushin Boko Haram da sauran ’yan ta’adda da ke dajin gami da bayar da dama ga masu son mika wuya su yi hakan. Janar Haruna ya bayyana fatansa na cewa karin ’yan ta’adda za su mika wuya, inda ya bayyana yadda suke ci gaba da mika wuya ga sojoji. “Kokarin da muke yi shi ne mu tabbatar da cewa mun kawar da ragowar ’yan ta’adda a Sambisa, tare da bai wa masu son mika kansu damar yin hakan. “Da wannan aiki, muna sa ran da yawa daga cikinsu za su mika wuya

Za Mu Sa Kafar Wando Da Masu Ambato Juyin Mulki — Sojoji

Image
Rayuwa ta yi tsada a Najeriya, lamarin da ya sanya wasu fara kiranye-kiranye da sojoji su yi juyin Rundunar Sojin Najeriya ta gargadi masu kiraye-kirayen juyin mulki, sakamakon matsalar tsaro da kuma tsadar rayuwa da ake fuskanta a fadin kasar nan. Najeriya dai na fuskantar matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa mafi muni a tarihi, abin da ya haifar da zanga-zanga a wasu sassan kasar nan. Wasu daga cikin ’yan kasar sun jima suna kiraye-kirayen sojoji su kifar da gwamnatin Tinubu tare da karbe iko kamar yadda aka yi a Jamhuriyar Nijar. Sai dai Daraktan Tsaro na Sojin Najeriya, Janar Christoper Musa, ya ce masu wannan kiraye-kiraye ba sa nufin kasar da alkahairi. Kazalika, dakarun sojin Najeriya za su sa kafar wando daya da masu wannan kiranye-kiranye. Ya ce abin da sojoji za su yi a yanzu shi ne kawai duba hanyoyin samar da sauki da kuma ciyar da kasar gaba, amma ba maganar juyin mulki ba. Da yake amincewa da halin matsi da ’yan Najeriya ke ciki, Janar Musa, ya ce babu inda juyin mulki