Posts

Showing posts with the label Yan Sanda

Nan Gaba Kadan Za A Gurfanar Da Ali Madaki A Kotu

Image
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta bayyana cewa cikin kankanin lokaci za ta gurfanar da zababben Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Dala a karkarshin tutar Jam’iyar NNPP, Honorabil Aliyu Madaki. Dan Majalisar dai ya shafe kawamaki biyu a hannun ’yan sanda kamar yadda kakakin rundunar ’yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatarwa Aminiya. Atiku zai garzaya kotu kan zaben shugaban kasa Yau Kotun Koli za ta ci gaba da shari’ar sauyin kudi Ana dai zargin Honorabul Aliyu Madaki da laifin fito da makami a fili wanda zai iya zama barazanar ga zaman lafiyar al’ummar jihar. An tsare Aliyu Madaki ne washegarin da rundunar ta cafke Shugaban Masu Rinjaye na Majaslisar Tarayya, Honorabul Alhassan Ado Doguwa. ’Yan sanda sun cafek Doguwa ne kan zargin tayar da zaune tsaye da kuma harin da aka kai Ofishin Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) a Karamar Hukumar Tudunwada ta Jihar Kano a lokacin da ake tattara sakamakon zaben shugaban kasa da na Majalisar Tarayya. Ana kuma al

Hukumar 'Yan Sanda Ta Kano, Ta Tsare Zababben Dan Majalisar Tarayya, Ali Madaki Bisa Fitowa Da Bindiga A Yayin Yakin Neman Zabe

Image
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tsare wani zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Dala ta jihar Kano a karkashin jam’iyyar New Nigerian Peoples Party, NNPP, Aliyu Madaki. DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa Mista Madaki ya karrama wata gayyata da ‘yan sanda suka yi masa a ranar Larabar da ta gabata bayan hotonsa na bidiyo yana dauke da bindigar famfo a lokacin wani gangamin dawowa gida na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP Rabi’u Kwankwaso, ya bayyana a yanar gizo. Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa wasu ‘yan daba sun kai hari kan ayarin motocin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a kan titin Zaria, Kano a ranar 23 ga watan Fabrairu a babban taron yakin neman zabensa na shugaban kasa, kuma ana zargin Mista Madaki ya jagoranci murkushe barayin. Lamarin ya kai ga cafke shugabannin jam’iyyar APC mai mulki na kananan hukumomin Ungogo da Rimingado a jihar Kano, Abdullahi Ramat da Munir Dahiru da bindigu da jami’an tsaro na hadin gwiwa suka yi. Dag