Posts

Showing posts with the label Rabon tallafin kudi

Kofa Ya Raba Tallafin Kudi Ga Mata Guda Dari Biyar A Mazabarsa

Image
A ci gaba da tagomashin arzikin da yake yi wa mutanen mazaɓarsa, Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan Majalisar Wakilai na Kiru da Bebeji daga jihar Kano, a ranar Lahadi ya sake gwangwaje mata 500 da tallafin kuɗi. A sanarwar da h adimin ɗan majalisar kan yaɗa labarai, Sani Ibrahim Paki  ya fitar, yace an  yi taron rabon tallafin ne a mahaifar ɗan majalisar da ke Kofa a Ƙaramar Hukumar Bebeji, Kano, kuma wannan shi ne karo na bakwai da yake raba irin wannan tallafin a ’yan makonnin nan.  Idan za a iya tunawa, a baya ɗan majalisar ya raba tallafin ga shugabannin al’umma, mata da matasa, ɗalibai, ’yan social media, malamai da masu rike da sarautun gargajiya.  Wannan ne dai rabon tallafi karo na bakwai tun bayan farawa, kuma karo na biyu ga mata. Bugu da ƙari, ɗan majalisar ya karɓi baƙuncin fitacciyar ’yar asalin Bebejin nan, kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Hajiya Azumi Babeji, wacce ita ma ta halarci bikin sannan ta gabatar masa da takardar nadin da Gwamnatin Jiha