Search This Blog

Showing posts with label Mele Kyari. Show all posts
Showing posts with label Mele Kyari. Show all posts

Tuesday, 18 July 2023

Yanayin Kasuwa Ne Ya Sa Man Fetur Ya Kara Tashi — NNPC

Shugaban Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, ya danganta tashin farashin man fetur daga Naira 540 zuwa Naira 617 da yanayin kasuwa.

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Talata, bayan wata ganawa da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.


“Farashin ya danganta da yanayin kasuwa. Wannan shi ne ma’anar tabbatar da cewa kasuwa ta daidaita kanta. Farashin zai iya hawa kuma a wani lokacin zai iya sauka. Ba batun samar da mai ba ne.

“Idan ka je kasuwa, ka sayi kaya, za ka zo kasuwa ka sayar da shi a kan farashin da kasuwa ta ke. Ba shi da alaka da wadatarsa. Mun samu sama da kwanaki 32 muna shigo da mai. Wannan ba matsala ba ce,” in ji shi.

Kyari, ya ce abu ne mai kyau ga ‘yan kasuwa su daidaita farashin.

“Ina tabbatar wa ’yan Najeriya cewa wannan ita ce hanyar da ta dace don daidaita farashin yanayin kasuwa. Ba ni da cikakken bayanai a wannan lokacin, amma na san cewa wannan ba mai dorewa ba ne. Na san cewa kamfanoni da yawa sun shigo da man fetur kuma komai zai daidaita nan bada jimawa.”

Martanin nasa na zuwa ne baya da wasu gidajen man NNPC aka wayi gari sun kara farashin man fetur daga 540 zuwa 617 a Abuja.


A nasa bangaren, babban jami’in hukumar kula da harkokin man fetur ta kasa, Farouk Ahmed, ya ce karin farashin ya faru ne sakamakon tashin farashin danyen mai.

Ya kuma ba da misali da sauye-sauyen farashin kaya tare da wasu karin kudadeen da masu shigo da kaya ke yi.

“Don haka, idan kuka ce yanayin kasuwa ya yi aiki, wannan shi ne ainahin abin da ake nufi, ya hau ko ya sauka… Kuna ganin farashin danyen mai ya tashi.

“Cikin mako daya farashin danyen mai ya kai kusan Dala 70 kan kowace ganga. Yanzu, yana kan Dala $80 kowace ganga.


“Don haka, babu shakka farashin danyen mai ne haifar da karin farashin kayayyaki. Kamar yadda masu shigo da kayayyaki ke shigo da su, suna dogara ne akan farashin shigo da kayayyaki da sauran abubuwan kashe kudi ta fuskar rarraba su a cikin gida,” cewar Ahmed.

A ranar Talata ne ‘yan kasuwa mai masu zaman kansu suka tabbatar da karin farashin man fetur, yayin da suka bayyana cewa duk wani canjin farashin da gidajen man NNPC suka yi na nuni da tashin farashin man.

A jawabinsa na farko a ranar 29 ga watan Mayu, shugaba Bola Tinubu ya sanar da dakatar da tallafin man fetur.

Wannan ya haifar da hauhawar farashin man fetur daga Naira 198 kan kowace lita zuwa sama da Naira 500 kan kowace lita a ranar 30 ga Mayu, 2023.
(AMINIYA) 


Saturday, 14 January 2023

A Watan Maris Za A Fara Hako Man Fetur A Jihar Nasarawa – NNPC

Kamfanin Mai na Najeriya (NNPC) ya ce a watan Maris Mai zuwa zai fara aikin hako danyen man fetur a karo na farko a Jihar Nasarawa.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari ne ya bayyana hakan ranar Juma’a, lokacin da ya karbi Gwamnan Jihar, Injiniya Abdullahi Sule da kuma wata tawaga daga Jihar a ofishinsa.

Gano man a rijiyar Keana ta Yamma da ke Jihar ta Nasarawa na zuwa ne kasa da wata biyar bayan kamfanin ya fara hakar wani a rijiyar Kolmani da ke tsakanin Jihohin Bauchi da Gombe.


A cikin sabuwar sanarwar da ya fitar ranar Juma’a, NNPC ya ce, “A ci gaba da aikinsa na gano man fetur a yankunan tsandauri na Najeriya, kamfanin zai fara aikin hako mai a rijiya ta farko a Jihar Nasarawa a watan Maris na 2023.”


Jaridar Aminiya ta ruwaito} Mele Kyari ya ce sakamakon binciken da suka gudanar ya tabbatar da akwai man fetur din dankare a yankin.

Daga nan sai ya bukaci a gaggauta fara aikin saboda ya ce sannu a hankali duniya ta fara dawowa daga rakiyar man fetur zuwa makamashin da ba ya lalata muhalli.

“Dole a gaggauta fara aikin nan saboda komai yanzu na sauyawa a duniya. Nan da shekara 10 ba lallai ne kowa ya yarda ya zuba jarinsa a harkar man ba matukar ba ya san zai ci riba ba. Saboda haka idan muka fara da wuri, ina ganin zai fi,” in ji Mele Kyari.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...