Search This Blog

Showing posts with label Diezani. Show all posts
Showing posts with label Diezani. Show all posts

Wednesday, 23 August 2023

Birtaniya Ta Gurfanar Da Diezani A Gaban Kotu Kan Zargin Almundahana

Kasar Birtaniya ta gurfanar da tsohuwar Ministar Man Fetur ta Najeriya, Diezani Alison-Madueke a gaban kotu kan zargin rashawa lokacin da take Minista.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa ’yan sandar kasar sun ce sun maka ta a kotun ne saboda suna zargin ta karbi cin hanci a wasu kwangilolin man fetur da iskar gas.

Diezani, mai shekara 63 a duniya, na daya daga cikin kusoshi a gwamnatin tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan.

A zamanin mulkin tsohon Shugaban, Diezani ta rike mukamin Ministar Mai ta Najeriya daga 2010 zuwa 2015, sannan ta rike matsayin shugabar Kungiyar Kasashe Masu Arzikin Man Fetur ta Duniya (OPEC).


A cewar Shugaban Hukumar Yaki da Laifuffuka ta Birtaniya (NCA), Andy Kelly, “gurfanarwar da aka yi wa Diezani wata somin-tabi ce na wani zuzzurfan bincike na kasa da kasa da aka dade ana yi.”

Hukumar dai ta ce ana zargin Diezani da karbar akalla tsabar kudi har Fam din Ingila 100,000 da wasu motoci da hawa jirgin da ba na ’yan kasuwa ba, yin hutun kece raini ita da iyalanta da kuma yin amfani da gidaje masu yawa a birnin Landan.

An kuma zarge ta da nuku-nuku kan wasu kadarori masu tsada da ta mallaka da suka hada da kayan ɗaki da biyan kudin makarantar ‘ya’yanta da kuma wasu sarkoki da kayan ado.
(AMINIYA)

Thursday, 12 January 2023

Mutum 26 Sun Saye Kadarorin Diezani Da Aka Yi Gwanjonsu


Akalla mutum 26 ne suka saye kadarorin da gwamnati ta yi gwanjonsu bayan kwato su daga hannun barayin gwamnati.

Kadarorin sun hada da gidaje da filaye da aka kwato daga tsohuwar Ministar Man Fetur, Diezani Allison-Madueke, a Abuja da sauran wurare.

A shekarar da ta gabata Hukumar Yaki da Rashawa (EFCC) ta yi gwanjon kadarorin ga masu son sayen su.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, a ranar Litinin hukumar ta fara mika kadarorin da aka saye na Legas da Abuja da Fatakwal da Kano da sauran wurare.

Sai dai kadarorin sun yi kwantai a ranar Liinin da aka yi gwanjon su, ko mutum guda ba a samu da ya sayi ko da daya daga cikinsu ba.

Amma mutum shida daga cikin 90 da suka nema suka yi nasara a rukuni na hudu a ranar Talata.

Da yake sanar da wadanda suka yi nasara a ranar Alhamis, mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren, ya ce kadarori 26 sun samu shiga, 13 kuma sun gaza, saboda rashin cika ka’ida da sauransu.

A cewar Uwujaren, “Kadarori 39 ne a rukuni na biyar wadanda ke a wurare daban-daban a cikin Abuja.”


A cewar Uwujaren, “Kadarori 39 ne a rukuni na biyar wadanda ke a wurare daban-daban a cikin Abuja.”
Ya ce za a sake bude kofa don bai wa mabukata su sayi kadarorin da suka rage a rukuni na biyar.

Da yake jawabi tun da farko, Shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, wanda a gabansa komai ya gudana ya ce, hukumar ta yi aiki tare da masana harkokin gidaje don tabbatar da ba a sayar da wata kadara kasa da darajarta ba.

“Yadda muka tafiyar da tasarin haka lamarin yake a kasashen duniya.

“Muna da masana kadarori da suka tantance mana darajar kowace kadara, kuma muna sa ran sallama wa wanda ya biya fiye da saura.

“Saboda muna da bukatar tara wa Gwamnatin Tarayya kudi don aiwatar da sabbi da kammala wasu manyan ayyukan da ke gabanta a sassan kasa.

“Mun samu korafe-korafen jama’a kan dalilin rashin gudanar da shirin ta intanet. Mun jarraba haka, amma sai muka zabi tsarin da zai ba mu damar yin komai a bayyane don ’yan kasa su shaida,” in ji Bawa.

Daya daga cikin wadanda suka samu nasarar mai suna Chetanna Chukwudo, ya bayyana jin dadinsa tare da kira ga EFCC da ta ci gaba da kyakkyawan aikin da ta sa gaba saboda ’yan kasa na tsumayar kyakkyawan cigaba daga gare ta.

Sunday, 25 December 2022

EFCC Ta Yi Gwanjon Kadarorin Su Diezani A Kasuwa


Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta sanar da yin gwanjon wasu kadarorin da ta kwace daga hannun ’yan siyasa da ’yan kasuwa ga ’yan Najeriya masu bukatar saya.

Hukumar ta ce kadarorin dai na jibge ne a Jihohin Legas da Ribas da Abuja da Anambra da Gombe da Ebonyi da Kaduna da Delta da Edo daKwara da Kuros Riba da Osun da kuma Oyo.

Aminiya ta gano cewa daga cikin kadarorin har da na tsohuwar Ministar Man Fetur ta Najeriya, Diezani Allison-Madueke, wadanda hukumar ta ce an mallake su ta haramtacciyar hanya.

A wata sanarwar da hukumar ta wallafa ranar Asabar, EFCC ta ce daidaikun mutane da kuma kamfanoni da kungiyoyin da ke son sayen kayan da aka yi gwanjon dole ne su kasance ba a taba daure su ba a baya.

Kadarorin da aka yi gwanjon nasu sun hada da wani gida a rukunin gidaje na Heritage Court a Jihar Ribas da wani mai daki uku a rukunin gidaje da ke rukunin gidaje na Foreshore a unguwar Ekoyin Jihar Legas fa sauran su.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...