Search This Blog

Showing posts with label Jami'a. Show all posts
Showing posts with label Jami'a. Show all posts

Friday, 14 February 2025

Abdulmumin Kofa ya Gabatar da kudirin kafa Jami'a a Kofa da Karin wasu Kudurorin 14

Abdulmumin Jibrin Kofa PhD, ɗan Majalisar Wakilai na mazaɓar Kiru/Bebeji, Kano, ya kafa tarihin gabatar da kudurori har guda 15 a zauren majalisar, kuma tuni dukkansu suka tsallake matakin karatu na farko a cikin mako ɗaya. 

Daga cikin ƙudurorin har da na kafa Jami’ar Kasuwanci ta Kofa, Bebeji, Kano, wanda shi tuni ya tsallake matakin karatu na biyu, Sannan akwai wasu ƙudurorin da suka shafi yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, bunƙasa harkokin zuba jari da kasuwanci, bayar da ilimin kyauta da kuma ilimin gaba da sakandare da dai sauransu. 
Ɗan Majalisar dai ya ɗauki lokaci sosai wajen yin nazari mai zurfi kan buƙatun mutanen mazaɓarsa, kafin ya gabatar da ƙudurorin a majalisa.

Jami’ar Kasuwancin za ta kasance irinta ta farko wajen horar da jajirtattun matasanmu su kasance maso dogaro da kai a harkar kasuwanci, ta yadda za su yi shi bisa ilimi sannan su yi gogayya da takwarorinsu a kasuwannin ciki da wajen Najeriya. 
Kano dai ita ce babbar cibiyar kasuwanci a Najeriya, inda take kafaɗa da kafaɗa da Jihar Legas. Saboda haka, amfanin wannan jami’ar ga mazaɓar Kiru/Bebeji, Jihar Kano da Najeriya baki ɗaya, ba zai misaltu ba. 
Ɗan Majalisar ya ce zai ci gaba da yin duk ƙoƙarinsa wajen kawo romon Dimokuraɗiyya ga yankin Kiru/Bebeji, Kano da Najeriya baki ɗaya.

Ga jerin kudurori 15 ɗin da ɗan majalisar ya gabatar a gaban majalisa.


Monday, 3 April 2023

Gwamnatin Kano ta nada Oba Balogun Da Farfesa Jega, Shugaba Da Uban Jami’ar Sa’adatu Rimi

Majalisar zartarwar jihar Kano ta amince da nadin Oba Dr. Sanata Moshood Olalekan Ishola Balogun Aliiwo da Farfesa Attahiru Jega, tsohon mataimakin shugaban jami’ar Bayero kuma tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa a matsayin Shugaban da Uban majalisar gudanarwar Jami'ar Ilimi ta Sa'adatu

Hakan ya biyo bayan samun amincewa ne daga Hukumar Kula da Jami’o’i ta kasa (NUC), wacce ta amince da ita a matsayin jami’ar Jiha ta 61 daga cikin jami'o'in guda 222 a tsarin jami’o’in Najeriya.

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba, wanda ya bayyana haka bayan taron majalisar da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin Kano ya bayyana sauran mambobin majalisar da suka hada da Dr. Muhammad Adamu Kwankwaso, Hajiya Zulaiha UM Ahmed, Dr. Ibrahim Yakubu Wunti, Dr. Halima Muhammad da Alhaji Sabi'u Bako.
 
Ya ce nadin ya zo daidai da sashe na uku na 22 na dokar Jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi ta Kumbotso wadda ta ce “za a yi majalisar da za ta zama hukumar gudanarwar jami’ar”, yayin da sashi na 1, 2 da 3. A cikin jadawalin na biyu na dokar ya tanadi cewa “bako, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje zai nada Chancellor, Pro Chancellor/Chairman of the Council da kuma na waje na majalisar.”
 
Malam Garba ya kara da cewa kamar yadda sashe na 3(2) na jaddawali na biyu, Pro Chancellor da sauran Yan majalisar gudanarwar Jami'ar za su ci gaba da rike mukaman na tsawon shekaru 4, wanda za a sabunta su na biyu kuma na karshe na wasu shekaru hudu.

A halin da ake ciki, bisa tsarin doka sashi na 5 da na biyu, majalisar ta baiwa maziyartan, Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin sabuwar jami’a a karon farko, amincewar nada manyan jami’ai da masu ziyarar Jami'ar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya nada. Ganduje, wanda shi ne zai jagoranci tafiyar da jami’ar.

Ya ce wadanda aka nada sune Farfesa Isa Yahaya Bunkure, Provost Sa’adatu Rimi College of Education (SRCOE), Kumbotso, mataimakin shugaban jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi; Dr. Kabiru Ahmad Gwarzo, mataimakin shugaban mai lura da harkokin koyarwa,  mataimakin shugaban jami’ar mai lura da harkokin mulki ; Dr. Miswaru Bello,  Saminu Bello Zubairu, a matsayin Maga takarda, Ibrahim Muhammad Yahaya, Bursar, SRCOE, Kumbotso, Mai Lura Da Harkokin kudi da kuma Mabruka Abubakar Abba a matsayin shugabar sashen lura da dakin karatu na jami'ar 

Kwamishinan ya bayyana cewa, yayin da nadin mataimakin shugaban jami’ar, magatakarda, mai kula da harkokin kudi da kuma mai lura da dakin karatu na tsawon shekaru biyar ne, mataimakin mataimakin shugaban jami’ar a fannin koyarwa, da na fannin mulki tsawon shekaru hudu kowannensu

Monday, 9 January 2023

An kori Farfesa daga aiki saboda nuna zanen hoton Annabi lokacin koyarwa

Jami’ar Hamline da ke birnin Minnesota na Amurka, ta kori wata Farfesa, Erika López-Prater, saboda nuna zanen Annabi Muhammad (S.A.W) yayin da take koyarwa.

A cewar rahotanni, wata daliba ce a ajin da take koyarwar ta yi korafi ga hukumar jami’ar.

An yi garkuwa da tsohon dan Majalisa a Edo
Isra’ila ta ba da umarnin cire tutocin Falasdinu daga gine-ginen gwamnati
Dalibar, mai suna Aram Wedatalla, ta shaida wa jaridar makarantar cewa ranta ya yi matukar baci da abin da malamar ta yi.

Aram dai wacce ’yar asalin kasar Sudan ce ta kuma ce ba za ta taba yarda ta zauna a cikin duk al’ummar da ba za ta mutunta abubuwan da ta yi amanna da su ba.


“A matsayina na Musulma kuma bakar fata, bana tunanin zan taba sakin jiki da kowacce irin al’ummar da ba ta mutunta ni kamar yadda nake mutunta ta,” inji ta.

Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito cewa Farfesar mai shekara 42, ta yi katobarar ce yayin wani ajin da take koyar da Tarihi, kodayake ta ce ta yi matukar taka-tsatsan kafin nuna zanen ga daliban.

Sai dai ta ce tun gabanin fara koyar da darasin, ta sanar da cewa za ta nuna hotunan Annabawa da sauran abubuwa masu tsarki, ciki har da na Musulmai da na addinin Buddha, kuma ta tambayi duk mai korafi a kai ya sanar da ita, amma babu dalibin da ya yi hakan.

Farfesar ta kuma ce ko a ajin ma, sai da ta sanar cewa za ta nuna hotunan na wasu ’yan mintuna, ko da wani daga cikin daliban na son ficewa saboda kada ya gani.


Sai dai malamar ta yi ikirarin cewa ba ta nuna hotunan domin cin zarafin Musulunci ba, inda ta ce hatta hotonta sai da ta nuna a lokacin da take dalibar jami’a a cikin ajin.



Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...