Posts

Showing posts with the label Jami'a

Abdulmumin Kofa ya Gabatar da kudirin kafa Jami'a a Kofa da Karin wasu Kudurorin 14

Image
Abdulmumin Jibrin Kofa PhD, ɗan Majalisar Wakilai na mazaɓar Kiru/Bebeji, Kano, ya kafa tarihin gabatar da kudurori har guda 15 a zauren majalisar, kuma tuni dukkansu suka tsallake matakin karatu na farko a cikin mako ɗaya.  Daga cikin ƙudurorin har da na kafa Jami’ar Kasuwanci ta Kofa, Bebeji, Kano, wanda shi tuni ya tsallake matakin karatu na biyu, Sannan akwai wasu ƙudurorin da suka shafi yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, bunƙasa harkokin zuba jari da kasuwanci, bayar da ilimin kyauta da kuma ilimin gaba da sakandare da dai sauransu.  Ɗan Majalisar dai ya ɗauki lokaci sosai wajen yin nazari mai zurfi kan buƙatun mutanen mazaɓarsa, kafin ya gabatar da ƙudurorin a majalisa. Jami’ar Kasuwancin za ta kasance irinta ta farko wajen horar da jajirtattun matasanmu su kasance maso dogaro da kai a harkar kasuwanci, ta yadda za su yi shi bisa ilimi sannan su yi gogayya da takwarorinsu a kasuwannin ciki da wajen Najeriya.  Kano dai ita ce ba...

Gwamnatin Kano ta nada Oba Balogun Da Farfesa Jega, Shugaba Da Uban Jami’ar Sa’adatu Rimi

Image
Majalisar zartarwar jihar Kano ta amince da nadin Oba Dr. Sanata Moshood Olalekan Ishola Balogun Aliiwo da Farfesa Attahiru Jega, tsohon mataimakin shugaban jami’ar Bayero kuma tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa a matsayin Shugaban da Uban majalisar gudanarwar Jami'ar Ilimi ta Sa'adatu Hakan ya biyo bayan samun amincewa ne daga Hukumar Kula da Jami’o’i ta kasa (NUC), wacce ta amince da ita a matsayin jami’ar Jiha ta 61 daga cikin jami'o'in guda 222 a tsarin jami’o’in Najeriya. Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba, wanda ya bayyana haka bayan taron majalisar da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin Kano ya bayyana sauran mambobin majalisar da suka hada da Dr. Muhammad Adamu Kwankwaso, Hajiya Zulaiha UM Ahmed, Dr. Ibrahim Yakubu Wunti, Dr. Halima Muhammad da Alhaji Sabi'u Bako.   Ya ce nadin ya zo daidai da sashe na uku na 22 na dokar Jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi ta Kumbotso wadda ta ce “za a yi ...

An kori Farfesa daga aiki saboda nuna zanen hoton Annabi lokacin koyarwa

Image
Jami’ar Hamline da ke birnin Minnesota na Amurka, ta kori wata Farfesa, Erika López-Prater, saboda nuna zanen Annabi Muhammad (S.A.W) yayin da take koyarwa. A cewar rahotanni, wata daliba ce a ajin da take koyarwar ta yi korafi ga hukumar jami’ar. An yi garkuwa da tsohon dan Majalisa a Edo Isra’ila ta ba da umarnin cire tutocin Falasdinu daga gine-ginen gwamnati Dalibar, mai suna Aram Wedatalla, ta shaida wa jaridar makarantar cewa ranta ya yi matukar baci da abin da malamar ta yi. Aram dai wacce ’yar asalin kasar Sudan ce ta kuma ce ba za ta taba yarda ta zauna a cikin duk al’ummar da ba za ta mutunta abubuwan da ta yi amanna da su ba. “A matsayina na Musulma kuma bakar fata, bana tunanin zan taba sakin jiki da kowacce irin al’ummar da ba ta mutunta ni kamar yadda nake mutunta ta,” inji ta. Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito cewa Farfesar mai shekara 42, ta yi katobarar ce yayin wani ajin da take koyar da Tarihi, kodayake ta ce ta yi matukar taka-tsatsan kafin nun...