Posts

Showing posts with the label Najeriya Kano

Yan sanda a jihar Kano sun kame 'yan daban siyasa fiye da 60

Image
‘Yan sanda a jihar Kano sun sanar da kame ‘yan daban siyasa akalla 61 yayin wani sumame da suka kaddamar a kokarin kakkabe barazanar rashin tsaro da aikata laifukan da ke ci gaba da tsananta a sassan jihar. Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mr Mamman Dauda da ke bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Haruna ya rabawa manema labarai, ya ce matakin kame ‘yan daban umarni ne daga babban sufeton ‘yan sandan kasar Usman Alkali-Baba. A cewar sanarwar galibin kamen an yi shi ne yayin gangamin siyasar da ke ci gaba da gudana a sassan jihar, a wani yunkuri na dakile barazanar ‘yan daban dai dai lokacin da babban zaben Najeriya ke ci gaba da karatowa. A Sanarwar da gidan Rediyon Faransa (RFI) ya wallafa a shafinsa, ta bayyana cewa ta hanyar tsaftace gari daga barazanar ‘yan daban siyasa ne kadai za a iya samun damar tafiyar da harkokin zaben da ke tunakarowa a wata mai zuwa. Rundunar ‘yan sandan ta jihar Kano ta ce ta gudanar da sumame ranar 4 ga wat