Posts

Showing posts with the label JAMB

Gwamna Abba Kabir Ya Kaddamar Da Rabawa Daliban Sakandare JAMB 6,500 Kyauta

Image
Ta hanyar samar da karin damammaki na neman ilimin manyan makarantu a jihar Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf a yau ya kaddamar da rabon fom din JAMB kyauta ga daliban makarantun sakandire 6,500 a wani taron da ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati Kano. Cikin wata sanarwa da kakakinsa Sanusi Bature Dawakin Tofa ya rabawa manema labarai ya nakalto Gwamnan a lokacin da yake kaddamar da rabon tallafin yana mai cewa, “Yayin da muke raba fom din JAMB kyauta a yau ga ‘yan jihar Kano 6,500, bari na tabbatar da hakan alama ce ta jajircewar gwamnatinmu  alÆ™awarin saka hannun jari a makomar yaranmu “Mun yi imanin cewa ilimi ginshikin ci gaba ne, kuma idan aka ba wa dalibanmu ilimi, yaranmu za su samu ilimi mai inganci, muna aza harsashin samar da ci gaba mai dorewa a jiharmu ta Kano.” Inji Gwamna Abba. Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen yin karin haske kan nasarorin da gwamnatinsa ta samu wajen bunkasa fannin ilimi a cikin watanni goma da suka hada da; sake daw

Zan mayar da Wa'adin Sakamakon JAMB Shekara 4 - Sanata Kwankwaso

Image
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP Rabiu Musa Kwankwaso yayi alkawarin tsawaita wa’adin sakamakon jarabawar shiga jami’a (JAMB) zuwa shekaru hudu idan ya ci zaben shugaban kasa. Majiyarmu ta rawaito cewa Kwankwaso ya bayyana hakan ne a Bauchi, lokacin da yake mika tutoci ga ’yan takarar gwamna shida da na Majalisar Dattijai 18 na yankin Arewa maso Gabashin Najeriya ranar Alhamis. An yi garkuwa da DPO a Filato Yadda aka yi wa Sakkwatawa kisan gilla a Anambra Kwankwaso ya ce dalibai da dama na samun sakamako mai kyau a rubuta jarabawar karo na farko, amma da zarar sun rasa gurbi a jami’a sai sun sake sabon lale bayan ba laifinsu ba ne. “Babu gaira babu dalili an sanya daliban da iyayensu lalubo kudin zana jarrabawa na shekaru biyu koma fiye. Haka ne ya sanya muku ga dacewar sauya haka. “Haka kuma za mu kirkiri sabuwar dokar dakatar da jarabawar JAMB din na tsawon shekaru hudu, domin ’ya’yanmu su yi amfani da sakamakon wajen samun gurbin karatu a manyan makarantun a w