Posts

Showing posts with the label BPE

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin 36 Sun Shiga Yarjejiniyar Sayar da Kamfanonin Wuta 5

Image
  A wata sanarwa da darekta janar na ofishin sayar da kaddarorin gwamnati wato BPE Alex Okoh ya fitar, ya nuna cewa za a sayar da kamfanonin wuta biyar a kwatan farko na wannan shekara da muka shiga, domin samar da kudade da za a cike gibin Kasafin kudin shekara 2023 da su.   Kasafin kudin na Naira Triliyan 21.82 ya zo da gibi har na kusan Naira triliyan 11 saboda rashin kudin shiga, haka ya sa aka samu gibin kashi 4.8 a ma'unin arzikin kasar wato GDP, wani abu da masanin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya nuna damuwa akan batun sayar da kamfanonin yana cewa akwai abin dubawa a wannan batun sayar da kamfanonin nan domin kar a sake fadawa cikin halin kakanakayi. https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/labari-da-dumiduminsa-yusuf-babangida.html https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/obasanjo-ya-zama-tamkar-dan-bakin-ciki.html Mikati ya ce haka aka sayar da kamfanoni ga wadanda ba su da kudi a zamanin gwamnatin da ta shude, har suka gagara ba kasa wadataccen wuta.