Posts

Showing posts with the label Kiru da Bebeji

Kofa Ya Raba Tallafin Kudi Ga Mata Guda Dari Biyar A Mazabarsa

Image
A ci gaba da tagomashin arzikin da yake yi wa mutanen mazaɓarsa, Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan Majalisar Wakilai na Kiru da Bebeji daga jihar Kano, a ranar Lahadi ya sake gwangwaje mata 500 da tallafin kuɗi. A sanarwar da h adimin ɗan majalisar kan yaɗa labarai, Sani Ibrahim Paki  ya fitar, yace an  yi taron rabon tallafin ne a mahaifar ɗan majalisar da ke Kofa a Ƙaramar Hukumar Bebeji, Kano, kuma wannan shi ne karo na bakwai da yake raba irin wannan tallafin a ’yan makonnin nan.  Idan za a iya tunawa, a baya ɗan majalisar ya raba tallafin ga shugabannin al’umma, mata da matasa, ɗalibai, ’yan social media, malamai da masu rike da sarautun gargajiya.  Wannan ne dai rabon tallafi karo na bakwai tun bayan farawa, kuma karo na biyu ga mata. Bugu da ƙari, ɗan majalisar ya karɓi baƙuncin fitacciyar ’yar asalin Bebejin nan, kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Hajiya Azumi Babeji, wacce ita ma ta halarci bikin sannan ta gabatar masa da takardar nadin da Gwamnatin Jiha

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Shirya Taron Addu'a Kan Nasarar Kotu, Ya Kuma Tallafa Wa Mutum 10,000

Image
Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Bebeji da Kiru, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya shirya taro na musamman wanda ya haɗa sama da mutum 10,000 domin yin addu’o’i a garinsa na Kofa da ke Karamar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano a ranar Lahadi  Ɗan majalisar mai hawa huɗu ya shirya taron ne domin ya gode wa Allah saboda nasarar da ya samu a Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da ta Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja a kwanakin baya, da kuma raba wasu kayan tallafi ga ’yan mazabarsa. A yayin kasaitaccen taron dai, an bayar da tallafi ga ’yan mazabar su 10,000 maza da mata. Bugu da ƙari, an ba mutanen tallafin kuɗi da kayan sanaa da motoci da kayan abinci da sutturu da kuma sauran kayan amfanin yau da kullum. Kazalika, an yi addu’a ta musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin neman Allah Ya ba shi nasara a Kotun Ɗaukaka Ƙara da ta Ƙoli, da sauran ’yan majalisar Kano na NNPP da suka yi nasara a kotu, da ma fatan nasara ga waɗanda ba a kai ga yanke