Posts

Showing posts with the label bincike

Gwamnan Kano Ya Nemi EFCC Ta Fitar Da Sakamakon Binciken Kwakwaf Da Ta Yi Kan Bidiyon Dala Na Ganduje

Image
Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mayar wa tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje martani, kan ikirarin gazawarsa a gwamnati mai ci, inda ya dage cewa wa’adin mulkin Ganduje na shekaru takwas na nuna gazawa da rashin gudanar da mulki, biyo bayan dimbin laifukan cin hanci da rashawa, karkatar da mulkin pf. kudade masu yawa da sayar da kadarorin gwamnati da suka siffantu da su. Gwamna Yusuf, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar kuma ya rabawa manema labarai. Lahadi, yayi nadamar cewa Ganduje cikin rashin kunya ya yi magana game da gazawar da babu ita a cikin New Nigeria Peoples. Gwamnatin Jam’iyyar (NNPP), maimakon ya fuskanci matsalar cin hanci da rashawa da tashe-tashen hankulan siyasa da suka rataya a wuyansa. Gwamna Yusuf ya dage cewa Ganduje ya shugabanci wasu wa’adin mulki guda biyu da ba su yi amfani da su ba, wadanda suka hada da wawure dukiyar al’umma, rashin iya biyan bukatun al’ummar Kano, son zuciya da zubar da jini w

Yin Waya Fiye Da Minti 30 A Sati Na Kara Hawan Jini —Bincike

Image
Masana kiwon lafiya sun gano cewa yin waya na sama da minti 30 a mako guda na haddasa karuwar cutar hawan jini da kashi 12. Rahoton da Kungiyar Likitocin Zuciya na Nahiyar Turai ta fitar a ranar Juma’a ya bukaci jama’a da su takaita yin waya domin kare lafiyar zukatansu. Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa rahoton likitocin da aka wallafa a mujallar  Digital Health  yana nuna yin waya na sama da minti 30 a mako na kara barazanar kamuwa da cutar hawan jina da kashi 12 cikin 100. Mujallar, wadda a mayar da hankali a kan yadda na’urorin zamani ke shafar lafiyar zuciya, ta ce hakan bai shafi yawan shekarun da mutun ya yi yana amfani da waya ko sanya waya a lasifika ba. Farfesa Xianhui Qin na Jami’ar Aikin Likita tat Kudancin Guangzhou da ke kasa China, ya kara da cewa masu amfani da waya sun fi mara sa yi yiwuwar kamuwa da hawan jini da kashi 7 cikin 100. Farfesa Qin ya a halin yanzu kusan biliyan 1.3 masu shekaru 30 zuwa 70 na da hawan jini, wadda ke iya kawo shanyew

Hisbah Ta Wanke Matar Da Ta Auri Saurayin ’Yarta A Kano Daga Zargi

Image
  Kwamitin da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kafa kan binciken auren matar da ta auri saurayin ’yarta, ya wanke ta daga zarge-zargen da ake mata. Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Alhaji Lawan Ibrahim ya fitar a Kano a ranar Talata. Sanarwar ta ce “Gabatar da rahoton binciken da kwamiti ya ya yi karkashin jagorancin Kwamanda Malam Hussain Ahmed, an gano auren halal ta yi kuma ta cika duk wasu sharuda da addini ya tanadar.” Sanarwar ta kuma ce bincikensu ya nuna cewar matar mijinta ya sake ta tun da fari kuma ta yi iddar wata uku kamar yadda addinin Musulunci ya tsara, kafin daga bisani ta auri saurayin ’yarta da ta daina so. Mataimakin Kwamandan ya yi watsi da zargin da ake wa matar na cewar ita ta kashe aurenta don ta auri saurayin ’yarta. “Auren halal suka yi kamar yadda Musulunci ya tsara, shi ya sa Kwamandan Hisbah a Karamar Hukumar Rano ya jagoranci daurin auren.” Babban Kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar, Harun Ibn-Sina, ya jinjina wa kwamitin kan yadda suka gudana