Posts

Showing posts with the label Kudin hajji

Labari Da Dumiduminsa: NAHCON Ta Sanar Da Kudin Hajjin 2024

Image
Idan dai za a iya tunawa da farko Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Malam Jalal Ahmad Arabi ya yi niyyar barin kudin aikin Hajjin 2024 a kan Naira miliyan 4.5 da aka karba a matsayin kudin ajiya tun farko.  A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, taceHasashen ya kasance mai girma har sai da batun kara karyewar darajar Naira ya faru a tsakiyar mako. Abin takaici, rashin tsayawa da aka samu a farashin Dala a baya-bayan nan ya tilasta yin gyare-gyaren da ya dace duk da kokarin da Shugaban Hukumar NAHCON, Jalal Ahmad Arabi ya yi na kula da farashin aikin Hajjin bana a kan wannan adadin.   A karshen watan Janairu ne shugaban Arabi ya tattauna kan samun rangwame mai yawa tare da masu ba da ayyukan Alhazai a masarautar Saudiyya, tare da kokarin rage farashin maniyyata aikin hajji. Sai dai kuma halin da ake ciki na tabarbarewar kudi a cikin satin, ya sa hukumar ta dauki tsattsauran mataki na ka

Hajjin 2024: Wajibi ne ga maniyyata su biya kuÉ—in Hajji nan da makonni 2- Shugaban hukumar alhazan Kebbi

Image
Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi, Alh Faruku Aliyu Yaro Enabo ya ja hankalin maniyyata a jihar da su hanzarta biyan kuÉ—in aikin Hajjin 2014 kafin nan da makonni biyu. Jaridar Hajj Reporters Hausa, ta rawaito cewa Enabo ya bayyana hakan ne a wata ganawa da yayi a yau Talata da Shuwagabannin Ƙananan Hukumomi 21 dake Jahar Kebbi a Babban Birnin Jahar, Birnin Kebbi. A cewar shi , biyan kudin kafin wa’adin makonni biyun shi zai tabbatar da cewa maniyyatan sun É—auki Æ™uduri na aikin Hajji. Ya Æ™ara da cewa Hukumar Alhazzai ta Ƙasar Saudiyya itace ta zo da sabbin tsare-tsare ta yadda dukkanin maniyyata za su samu biza kamin wata uku da tashi zuwa Ƙasa mai tsarki. Bayan gabatar da shuwagabannin Hukumar, Daraktoti da Masu Bawa Gwamna Shawara, Alh Faruku Enabo ya ja hankalinsu da su bawa maraÉ—a kunya, ya Æ™ara da cewa duk wanda aka samu da laifi babu makawa za’a É—auki matakin ladabtarwa. (Hajj Reporters Hausa)

Yakin Sudan: Akwai Yiwuwar Maniyyata Su Kara Biyan Wasu Kudin

Image
  Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tabbatar da cewa yaÆ™in da ake yi a kasar Sudan zai shafi jigilar maniyyatan Najeriya na bana, wanda ka iya sanadin karin kudin kujerar. A ranar Talata hukumar da kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar jigilar mahajjatan ta bana A makon jiya dai sun gaza yin hakan saboda batun Æ™arin kuÉ—i. Sai dai hukumar ba ta bayyana ko matakin na nufin, maniyyata aikin hajji ne za su biya Æ™arin kuÉ—in da dogon zagayen zuwa kasa mai tsarki ko a’a ba. Kwamishinan Tsare-tsare da Gudanar da Gikin Hajji a hukumar, Abdullahi Magaji Hardawa, ya ce har zuwa yanzu ba a cimma matsaya kan ko mahajjata ne za su yi Æ™arin kuÉ—in ba. A cewarsa, matuÆ™ar ba a buÉ—e sararin samaniyar kasar Sudan ba, har aka fara jigilar maniyyatan bana daga Najeriya, to dole sai jiragen sama sun yi zagaye, wanda zai haddasa Æ™arin kuÉ—i. Jami’in ya ce babban hatsari ne jirgin sama ya ratsa ta sararin samaniyar Sudan, shi ya sa hukumomin Æ™asar suka dakatar