Search This Blog

Showing posts with label Kudin hajji. Show all posts
Showing posts with label Kudin hajji. Show all posts

Saturday, 3 February 2024

Labari Da Dumiduminsa: NAHCON Ta Sanar Da Kudin Hajjin 2024

Idan dai za a iya tunawa da farko Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Malam Jalal Ahmad Arabi ya yi niyyar barin kudin aikin Hajjin 2024 a kan Naira miliyan 4.5 da aka karba a matsayin kudin ajiya tun farko. 

A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, taceHasashen ya kasance mai girma har sai da batun kara karyewar darajar Naira ya faru a tsakiyar mako. Abin takaici, rashin tsayawa da aka samu a farashin Dala a baya-bayan nan ya tilasta yin gyare-gyaren da ya dace duk da kokarin da Shugaban Hukumar NAHCON, Jalal Ahmad Arabi ya yi na kula da farashin aikin Hajjin bana a kan wannan adadin.
 
A karshen watan Janairu ne shugaban Arabi ya tattauna kan samun rangwame mai yawa tare da masu ba da ayyukan Alhazai a masarautar Saudiyya, tare da kokarin rage farashin maniyyata aikin hajji. Sai dai kuma halin da ake ciki na tabarbarewar kudi a cikin satin, ya sa hukumar ta dauki tsattsauran mataki na karfafa nasarorin da aka samu wajen rage farashin hidimar aikin Hajji, wanda idan ba tare da haka ba farashin aikin hajjin na shekarar 2024 zai iya zuwa kusan  Naira miliyan shida
 
Don haka, ana bukatar maniyyatan da suka fito daga yankin Kudancin Najeriya su biya N4,899,000 a matsayin kudin aikin Hajji; wadanda suka fito daga tsakiyar Arewa za su biya Naira miliyan 4,699,000, na aikin Hajji, kuma mahajjata daga Yola da Maiduguri za su biya Naira miliyan 4,679,000 na aikin Hajjin 2024.
 
Da yake bayyana nadamarsa, Shugaban Hukumar Arabi ya bayyana cewa, wannan nufin Allah ne, domin Hukumar, tana fuskantar tsaikon wa’adin ranar 25 ga watan Fabrairu, ta tanadi wasu zabukan da za su ci gaba da kasancewa a cikin iyakar Naira miliyan 4.5 da ya yi aiki da su. Don haka, NAHCON ta bayyana kudin da za a iya yi na aikin Hajji don cika wa’adin lokacin da ke tafe.
 
Don haka an shawarci maniyyatan da su cika ragowar kudinsu nan da zuwa ranar Litinin 12 ga watan Fabrairu don baiwa hukumar damar mika kudaden kafin cikar wa’adin.
 
Hukumar NAHCON tana tabbatar lwa al’umma kudurinta na ganin an gudanar da aikin hajji cikin nasara da duk da kalubalen da ke tattare da canjin kudaden kasashen waje. Hukumar ta yaba da fahimta da hadin kan al’ummar Musulmin Najeriya a wadannan lokuta.
 

Tuesday, 7 November 2023

Hajjin 2024: Wajibi ne ga maniyyata su biya kuɗin Hajji nan da makonni 2- Shugaban hukumar alhazan Kebbi

Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi, Alh Faruku Aliyu Yaro Enabo ya ja hankalin maniyyata a jihar da su hanzarta biyan kuɗin aikin Hajjin 2014 kafin nan da makonni biyu.

Jaridar Hajj Reporters Hausa, ta rawaito cewa Enabo ya bayyana hakan ne a wata ganawa da yayi a yau Talata da Shuwagabannin Ƙananan Hukumomi 21 dake Jahar Kebbi a Babban Birnin Jahar, Birnin Kebbi.

A cewar shi , biyan kudin kafin wa’adin makonni biyun shi zai tabbatar da cewa maniyyatan sun ɗauki ƙuduri na aikin Hajji.

Ya ƙara da cewa Hukumar Alhazzai ta Ƙasar Saudiyya itace ta zo da sabbin tsare-tsare ta yadda dukkanin maniyyata za su samu biza kamin wata uku da tashi zuwa Ƙasa mai tsarki.

Bayan gabatar da shuwagabannin Hukumar, Daraktoti da Masu Bawa Gwamna Shawara, Alh Faruku Enabo ya ja hankalinsu da su bawa maraɗa kunya, ya ƙara da cewa duk wanda aka samu da laifi babu makawa za’a ɗauki matakin ladabtarwa.

(Hajj Reporters Hausa)

Wednesday, 10 May 2023

Yakin Sudan: Akwai Yiwuwar Maniyyata Su Kara Biyan Wasu Kudin


 Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tabbatar da cewa yaƙin da ake yi a kasar Sudan zai shafi jigilar maniyyatan Najeriya na bana, wanda ka iya sanadin karin kudin kujerar.

A ranar Talata hukumar da kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar jigilar mahajjatan ta bana

A makon jiya dai sun gaza yin hakan saboda batun ƙarin kuɗi.

Sai dai hukumar ba ta bayyana ko matakin na nufin, maniyyata aikin hajji ne za su biya ƙarin kuɗin da dogon zagayen zuwa kasa mai tsarki ko a’a ba.

Kwamishinan Tsare-tsare da Gudanar da Gikin Hajji a hukumar, Abdullahi Magaji Hardawa, ya ce har zuwa yanzu ba a cimma matsaya kan ko mahajjata ne za su yi ƙarin kuɗin ba.

A cewarsa, matuƙar ba a buɗe sararin samaniyar kasar Sudan ba, har aka fara jigilar maniyyatan bana daga Najeriya, to dole sai jiragen sama sun yi zagaye, wanda zai haddasa ƙarin kuɗi.

Jami’in ya ce babban hatsari ne jirgin sama ya ratsa ta sararin samaniyar Sudan, shi ya sa hukumomin ƙasar suka dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a kasar.

Harɗawa ya ce matuƙar aka fara jigilar maniyyata aikin hajji na bana, ba tare da an bi ta Sudan ba, za a fuskanci matsaloli guda biyu ko fiye.

“Na farko, in ba za a shiga ta sararin samaniyar Sudan ba, dole za a shiga ta wasu ƙasashe. To ƙasashen nan akasari, za a biya su kuɗin ratsawa ta sararin samaniyarsu.

“To maimakon kuɗin da za a biya na ƙasa ɗaya, wato Sudan. (A yanzu) mai yiwuwa a biya na ƙasashe da yawa. Kun ga an samu ƙarin kuɗaɗe ke nan,” in ji shi.

Na biyu, a cewarsa, tun da akwai ƙarin tazara kamar na sa’a biyu a tafiyar jirgin sama, man da jirgin yake sha ma zai ƙaru, wanda ke nufin ƙarin kuɗin jigilar alhazai.

Abdullahi Harɗawa ya ce kamfanonin jiragen sama sun sa hannu a kan yarjejeniyar jigilar aikin hajjin na bana ne bayan an daddale tsakaninsu da Hukumar NAHCON a kan matsalolin da za a iya fuskanta.

Ya ce: “Sun amince sun sa hannu ɗin, amma an yarda akwai bukatar a san yadda za a yi, a ƙara musu farashi.”

Jami’in ya ce kasanceaw maniyyata sun riga sun biya kuɗi, “bisa yadda aka tallatar masa,”  yanzu ba zai iya tabbatar da ko za a bukaci maniyyaci ya kara biyan wasu kudin ba.

“Amma dai abin da nake tabbatar muku so hi ne, akwai bukatar ƙarin kuɗi. Akwai tazara da yawa. Akwai ɗawainiya da yawa. Karin kuɗin nan daga ina zai fito? Shi ne ba a cimma matsaya ba”.

Kamfanonin sufurin jiragen saman da suka sa hannu kan yarjejeniyar sun haɗar da – Air Peace da Azman Air Services da Aero Contractor da kuma Max Air.

AMINIYA

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...