Posts

Showing posts with the label Bazoum

Sojojin Nijar Za Su Gurfanar Da Bazoum Kan Zargin Cin Amanar Ƙasa

Image
Gwamnatin sojin Nijar ta sha alwashin gurfanar da hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum kan zargin babban cin amana da kuma zagon ƙasa ga sha’anin tsaron ƙasar. Masu juyin mulkin sun ce sun tattara hujjojin da za su yi amfani da su wajen gurfanar da Bazoum da kuma waɗanda suka kira muƙarrabansa na cikin gida da na ƙasashen waje. Ministan Matasa da Wasanni, Kanar-Manjo Amadou Abdraman ya sanar a talabijin a ranar Lahadi cewa za su gurfanar da Bazoum da muƙarraban nasa ne a cikin ƙasar Nijar da kuma gaban hukumomin da suka dace na duniya, kan babban cin amanar ƙasa da yin zagon ƙasa ga tsaron Jamhuriyar Nijar. Tun ranar 26 ga watan Yuli da sojojin suka yi wa Bazoum juyin mulki suke tsare da shi da matarsa da ɗansa a cikin gidansa. Shugabannin sojojin na iƙirarin cewa ba mamaye gidan nasa suka yi ba, domin kuwa yana ci gaba da mu’amala da sauran duniya, kuma likitansa na zuwa ya duba shi a kai a kai, yadda ya saba yi. Wani mashawarcin Bazoum ya tabbatar cewa a ranar Asabar

Juyin Mulkin Nijar: Ministan Bazoum Ya Nada Kansa Shugaban Gwamnati

Image
Minitsan harkokin wajen Jamhuriyyar Nijar, Hassoumi Massoudou ya ayyana kansa a matsayin Shugaban Gwamnati, yana mai kira ga al’ummar kasar su murkushe juyin mulkin da sojoji suka yi wa Shugaba Mohammed Bazoum. Kawo yanzu dai ba a san hanlin da Mista Bazoum yake ciki ba a hannun masu juyin mulkin. Amma wani sako da aka wallafa ta shafinsa na Twitter a safiyar Alhamis ya ce, “za a kare nasarar da ya samu” kuma al’ummar kasar ne za su tabbatar da hakan. Zargin kashe madugun juyin mulki? Wasu rahotanni daga kasar kuma na cewa sojojin sun kashe wanda ya jagorance su wajen yin juyin mulkin, Abdulrahman Chani. Shugaban gidan rediyon Amfani FM da ke birnin Yamai na kasar, Issoufu Mammane, ya shaida wa Aminiya cewa ana zargin an harbe shi har lahira ne a yayin takaddama kan wanda zai jagoranci gwamnatin sojin, wadda yake neman nada kansa. “A yayin jayayya saboda ya ce shi zai dauki mulki, su kuma sauran sojojin suka ce ba shi zai dauka ba ga wanda za ya dauka (Salifou Modi)… suna wannan