Search This Blog

Showing posts with label Beli. Show all posts
Showing posts with label Beli. Show all posts

Saturday, 9 August 2025

Gwamnan Kano Ya Sauke Hadimansa Guda Biyu Daga Mukaminsu

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf ta amince da korar manyan mataimaka biyu (Senior Special Assistants) nan take, bayan samun shaidu masu karfi daga rahotannin kwamitocin bincike da aka kafa kan wasu zarge-zargen aikata laifuka daban-daban.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ya fitar a ranar Asabar.

A cikin mataki mai tsauri, Gwamna Abba ya amince da korar Abubakar Umar Sharada, Mai taimaka masa na musammam kan Kan Hada kawunan yan siyasa bayan wani kwamitin bincike na musamman ya same shi da hannu wajen belin wani sanannen dillalin miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu, inda shaidar da Sharada ya bayar da kansa gaban kwamitin ta tabbatar da rawar da ya taka a wannan mataki na bayar da beli.

A wasikar da Sakataren Gwamnati ya fitar a ranar Juma’a, 8 ga Agusta, 2025, an umarci Sharada da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannunsa ga Babban Sakataren  na Sashen Bincike, Kimantawa da Harkokin Siyasa (REPA) a ofishin Sakataren Gwamnati kafin karshen lokacin aiki ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025.

Haka kuma, an gargade shi da kada ya sake yin ikirarin kasancewa jami’i  na gwamnati.

Haka nan, Gwamna Abba ya sallami Tasiu Adamu Al’amin Roba, Babban mataimaki na musammam a Ofishin Majalisar Zartarwa (Cabinet Office), bayan kama shi yana sake nade hatsi na Tallafin rage radadi a wani rumbun a Sharada a shekarar 2024.

Roba ya riga ya gurfana a kotu inda ake tuhumarsa da laifin sata da kuma hada baki wajen karkatar da dukiyar gwamnati.

Haka kuma, an umarce shi da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannunsa, ciki har da katin shaidar aiki, kafin ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, tare da gargadin kada ya sake yin ikirarin kasancewa jami’in gwamnati.

A wani labarin kuma, gwamnatin jihar ta wanke Mai bawa Gwamna kan harkokin Shawara kan Hanyoyin Ruwa, Hon. Musa Ado Tsamiya, bayan kwamitin bincike ya tabbatar da cewa bai da hannu a dukkan zarge-zargen da ake masa.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da tabbatar da ladabi, gaskiya da rashin sassauci kan cin hanci da rashawa, tare da gargadin cewa dukkan jami’an gwamnati su tabbatar suna aiki da nagarta a aikinsu da kuma rayuwarsu ta kashin kai.

Ta wannan sanarwa, an shawarci jama’a da kada su yi hulɗa da wadannan mataimaka biyu da aka kora kan duk wani lamari da ya shafi gwamnatin Jihar Kano, domin duk wanda ya yi hakan, to ya rage nasa.


Saturday, 6 May 2023

Zaben Adamawa: An Ba Da Belin Kwamishina Hudu

 


’Yan sanda sun bayar da belin Kwamishinan Zabe na Jihar Adamawa da aka dakatar, Hudu Yunusa-Ari, bayan da ya yi kwana uku a tsare a hannunsu.

’Yan sanda sun cafke shi ne kan wata sanarwa mai cike da rudani da ya yi  cewa Sanata Aisha Dahiru Binani ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa, alhali ba a kammala karbar sakamakon karashen zaben ba.

Tun a lokacin INEC ta soke sanarwar, sannan ta bukaci ya gabatar da kansa a hedikwatarta da ke Abuja, amma maimakon ya je, sai ya yi layar zana.

Daga bisani hukumar ta rubuta Shugaban ’Yan Sandan Najeriya wasikar neman ya binciki kwamishinan zaben, kan yamutsa hazon da ya yi.

Amma wata wasika da ya aike wa shugaban ’yan sanda, Hudu ya ce ya yi sanarwar ne a bisa doka, saboda dalilan tsaro.

A ranar Talala ’yan sanda suka sanar cewa sun kama Hudu, wanda ya ce ba ya nadamar sanarwar da ya ya yi cewa Binani ta ci zabe.

Amma kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Muyiwa Adejobi, ya sanar a ranar Juma’a cewa rundunar ta bayar da belin kwamishinan zaben.

Muyiwa ya cen an umarci Hudu ya rika zuwa hedikwatar rundunar a ranakun aiki domin ci gaba da binciken da ake gudarwa.

AMINIYA

Monday, 6 March 2023

Yanzu-Yanzu : Kotu Ta Bayar Da Belin Alasan Ado Doguwa

Kotun Magistare dake unguwar Nomansland a Kano, ta bayar belin Zababben Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar yankin kananan hukumomin Tudun Wada da Doguwa, Alhaji Alasan Ado Doguwa. 

Hakan ta faru ne biyo bayan neman bukatar hakan da lauyoyin sa suka gabatar. 

Za a iya tunawa cewa a makon da ya gabata ne jami'an tsaro suka kama Shugaban masu rinjaye na majalisar bisa zargin aikata laifukan da suka hada da kisa a yayin gudanar da zabe 

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...