Search This Blog

Showing posts with label Zamfara. Show all posts
Showing posts with label Zamfara. Show all posts

Monday, 27 April 2026

Allegations Against Former Zamfara Governor, Bello Matawalle Are Untrue - Fahad Ogan Boye

We wish to categorically respond to the series of allegations and defamatory statements being directed at the former Governor of Zamfara State and current Minister of State for Defence, Bello Matawalle.


In a statement signed by Fahad Ogan Boye, these claims are baseless, misleading, and driven by envy, hatred, and a calculated attempt to tarnish his hard earned reputation.


Let it be made unequivocally clear that we will not stand by while these unfounded accusations persist. Any individual or group found spreading falsehoods against him will be met with appropriate legal action.
It is important to recall that similar allegations were previously made, linking him to banditry activities claims which have since been proven to be entirely false and without merit.


His continued role and relevance within the administration of President Bola Ahmed Tinubu is a clear testament to his integrity, credibility, and commitment to national service.


Arabs says “If you want to know a person, look at his friends.” Nigeria’s security agencies are made up of professionals who uphold truth and justice. If there were any substance to these accusations, investigations would have been conducted and appropriate actions taken.


The absence of such findings further affirms that Bello Matawalle is a man of honor and integrity.


I extend our sincere appreciation to President Bola Ahmed Tinubu for the confidence and opportunities he has given to patriotic Nigerians like Bello Matawalle, who remain committed to the unity, progress, and security of our nation.


Therefore, I extend my gratitude to the Minister of defence Christopher Musa and National Security Adviser Malam Nuhu Ribado over their dedication in ensuring security and Stability in the nation under the of the President Bola Ahmad Tinubu.


I therefore call on all Nigerians to remain steadfast in supporting the leadership of President Bola Ahmed Tinubu as he continues to steer the country toward growth and stability.


Monday, 5 May 2025

Despite insecurity, Zamfara students excel at Savannah conference basketball in Kano

Despite the insecurity challenge, representative of Zamfara state in the ongoing Savannah Conference inter secondary schools basketball championship for boys and girls are in high spirit and make an impact in the tournament.

The head of school sports under the special services in the state ministry of education, Malam Sagir Sani stated this shortly after Sambo Secondary schools, Busau, and Government girls day secondary school, Samaru, Zamfara state walked over their opponents from Yobe state held at the indoor sports hall of Sani Abacha Sports Complex, Kofar Mata, Kano.

Malam Sagir Sani explained that his players (boys and girls) were gradually making efforts to ensure picking a point in the matches.

He described the performance of the players as highly impressive, calling on them to redouble efforts especially in projecting the good image of Zamfara as far as sports was concerned in the country.

While expressing gratitude to the the state Governor Dr Dauda Lawan and the state Commissioner of science and technology, Malam Wada Tau Madawaki as well as the Executive Chairman of Senior Secondary schools Education board for their total support morally and financially to the students.
Malam Sagir Sani who double as the NSSF's Public Relations officer assured that the coaches would go back to the drawing board to review the matches with a view to actualize their set objective.

However, he appealed to the state government as a matter of urgency to improve the schools various facilities aimed at developing the students' skills in future sporting events in the state and the country at large.

....As NSSF VP four hails participants, officiating officials


the Vice President four of the Nigerian School Sports Federation NSSF, Malam Aminu Sarkin Fada has applauded the participants for their commitment and sportsmanship in the championship.

He made the commendation in the ongoing Savannah Conference Nestle Milo basketball championship in Kano.

Malam Aminu Sarkin Fada said that the championship has contributed immensely to the development of the game in the country, assuring that the NSSF will do it's best to ensure more national and international players were produce in the tournament.

On officiating and general organisation, he expressed satisfaction with the performance of the referees and good facilities in Kano.

Today Tuesday is a free day as the NSSF is also organizing clinic for the participating coaches in order to improve their technical knowledge of the game from 8am to 11 am at the competition's venue, Kofar Mata. 

Four states have already qualified for the semi final of the competition namely Bauchi, Adamawa, Gombe and the host state Kano. The semi final will hold on Wednesday in the morning.
The winners for boys and girls in the Savannah conference will represent the zone in the stage of the championship scheduled to hold later in the year in Lagos.

Wednesday, 13 December 2023

Na shiga matsananciyar damuwa da hare-haren 'yan bindiga a 'yan kwanakin nan - Gwamnan Zamfara

Gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook

Inda yace "A madadin gwamnatin Jihar Zamfara, ina miƙa saƙon ta'aziyya da jaje ga al'ummar ƙaramar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan waɗanda suka rasa rayukansu a harin ta'addanci da 'yan bindiga suka kai garin" 

Ina son tabbatarwa da al'umma cewa gwamnatina za ta bayar da tallafi da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa. Sannan ina mai tabbatar da cewa muna nan jajirce akan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar Zamfara baki ɗaya.

Ina sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suke yi a ƙoƙarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatina za ta ba su duk wasu kayan aiki da kuma tallafin da suka dace domin yaƙar ‘yan bindiga, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro insha Allahu.
 
Waɗannan sabbin hare hare sun biyo bayan nasarar da jami'an tsaro suka samu ne, na kashe shugabannin 'yan ta'addan. Ciki har da nasarar kashe Kachalla Ali Kawaje, Shugaban ‘yan bindiga da ya jagoranci sace ɗaliban jami’ar tarayya dake Gusau.
 
An samu nasarar kawar da shugabannin ɓarayin da dama a wurare daban-daban da suka haɗa da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.
 
Ina sake jaddada wa al'ummar Jihar Zamfara cewa, da yardan Allah zan ci gaba da bin dukkan matakan da suka dace don tabbatar da zaman lafiya a faɗin jiharmu mai albarka.

Saturday, 29 April 2023

’Yan Bindiga Sun Sako 70 Daga Cikin Yara 85 Da Suka Sace A Zamfara

 


’Yan ta’adda da suka yi garkuwa da yara sama da 85 a Jihar Zamfara sun sako 70 daga cikin yaran, amma sun kashe biyu.

A ranar Juma’a ’yan ta’addan suka sako yaran, kimanin mako uku bayan sun sace su daga kauyen Wanzamai na Karamar Hukumar Tsafe ta jihar.

Wani mazaunin yankin Sani Aliyu ya ce, “Yara biyu da ’yan bindigar suka kashe sun yi kokarin tserewa ne, wadanda aka sako din kuma sun galabaita saboda tsananin yunwa, kuma yanzu ana duba lafiyarsu.”

Ya ce ganin irin galabaitan da yaran suka yi ya sa iyayensu koke-koke, kuma “An sako su ne bayan an biya kudin fansa Naira miliyan shida; da farko miliyan uku aka ba su, amma suka ki sako su, sai an kara musu da sabbin babura guda biyu.”

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bangaren Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, amma hakarsa ta yin magana da kakakin rundunar, CSP Muhammad Shehu, ba ta cim ma ruwa ba.

Kimanin makonni uku da suka gabata ne ’yan bindiga suka  ritsa wasu yara da suka je neman icen girki da wasu manya a gonaki suka yi awon gaba da su a yankin Tsafe na Jihar Zamfara.

Daga cikin manyan da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su har da mata.

AMINIYA

Monday, 6 March 2023

Tinubu Ya Yi Alawadai Da Harin 'Yan Bindiga A Zamfara, Kano Da Katsina is a Tare Da Jajantawa Wadanda Abun Ya Shafa

Tinubu ya kuma yi ta'azziya ga iyalan Abacha da na Sheikh Gumi 

Zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da hare-haren da ‘yan bindiga da wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara da kuma garin Maigari na karamar hukumar Rimin Gado a jihar Kano a karshen mako.
Rahotanni sun ce an kashe jami’in ‘yan sanda na Dibision (DPO), sufeto ‘yan sanda da dan banga a harin da ‘yan bindiga suka kai a Zamfara. A harin na Kano wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun shiga gidan wani basarake inda suka harbe shi har lahira.

A cikin wata sanarwa da ofishin yada labaran sa ya fitar a ranar Litinin, Tinubu ya ce harin da aka kai a garin Maru bayan an samu zaman lafiya a jihar Zamfara, abin tunatarwa ne cewa akwai bukatar a kara kaimi domin murkushe ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda gaba daya.

“A matsayinmu na kasa dole ne mu hada kai domin mu fatattaki wadannan ‘yan kasuwa na mutuwa da ta’addanci gaba daya, kashe-kashen rashin tunani da ta’addanci irin wannan bai kamata ya zama wani wuri a kasarmu ba,” inji shi.

Zababben shugaban kasar ya jajantawa Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, da gwamnatin jihar Zamfara da iyalan jami’an tsaron da abin ya shafa bisa rasuwar.

Tinubu ya kuma bukaci a gudanar da bincike kan kisan Hakimin Maigari a Jihar Kano, wanda shi ne mahaifin shugaban karamar hukumar Rimin Gado, Munir Dahiru Maigari.

Ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban karamar hukumar, gwamnatin jihar Kano da iyalan mamacin bisa mummunan kisan da aka yi wa shugaban al’umma.

A cikin sakon ta’aziyya daban-daban, zababben shugaban kasar ya jajantawa fitaccen malamin nan Sheikh Ahmad Gumi da ya rasa mahaifiyarsa tsohuwa da kuma iyalan marigayi Janar Sani Abacha bisa rasuwar dansu Abdullahi.

“Yana shafar rabuwa da masoyi komai yanayi da shekaru, ba za mu iya kokwanton nufin Allah ba sai dai kawai mu yi addu’a Allah Ta’ala ya ba su hutun dawwama, ya kuma ba mu karfin gwiwar jure wa rasuwarsu,” inji shi.

Zababben shugaban kasar ya jajantawa dukkan iyalan da suka rasa ‘yan uwansu tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.


Tuesday, 3 January 2023

Matawalle ya dakatar da yakin neman zaben APC a Zamfara

Gwamna Bello Mohammed Matawalle ya dakatar da yakin neman zaben Jam’iyyar APC a Jihar Zamfara har zuwa ranar 18 ga watan Janairu da muke ciki.

Rohotanni sun bayyana cewa kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar ya dakatar da harkkokin kamfe din gwamnan ne don mayar sa hankali kan zaman lafiya a jihar.

“Na yi alkawarin mayar da hankali wajen dawo da zaman lafiya a mulkina na biyu a Jihar Zamfara,” cewar Matawalle.

Aminiya ta ruwaito cewa Ya bayyana haka ne a lokacin da jam’iyyar ta kaddamar da yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Kaura Namoda, a ranar 27 ga watan Disamba, 2022.

Matawalle dai ya nada tsohon gwamnan jihar, Abdulaziz Yari a matsayin shugaban kwamitin yakin neman zabensa.

A nasa bangaren, tsohon gwamnan jihar ya ce matsalar tsaro za ta inganta idan Matawalle ya sake darewa kujerar mulkin jihar a karo na biyu.

Yari, wanda ya jagoranci kwamitin yakin neman zaben APC zuwa kamfe din jam’iyyar ya ce zai goyi bayan takarar Matawalle dari bisa dari.

Monday, 2 January 2023

’Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Kanar Din Soja A Zamfara

 


’Yan bindiga sun sace Kanar Lawal Rabiu Yandoto (mai ritaya) a kan hanyarsa ta zuwa garinsu, Yandoto da ke Karamar Hukumar Tsafe a Jihar Zamfara.

Wata majiya ta bayyana cewa ’yan bindigar sun sace shi ne tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu.

“Maharan sun yi wa Kanar kwanton bauna da misalin karfe 6 na yamamcin ranar Lahadi, suka sace shi tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu mutum biyu,”  in ji majiyar.

Majiyar ta ce an ji karar harbe-harbe daura da shiga garin na Yandoto lamarin da ya tilasta mutane guje-guje domin tsira.

Kakakin ’yan sandan jihar bai daga waya ba ballatana a ji ta bakinsa kan lamarin.

(AMINIYA)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...