Search This Blog

Showing posts with label satar mutane. Show all posts
Showing posts with label satar mutane. Show all posts

Thursday, 29 February 2024

'Yan Bindiga Sun Sace Mutum Talatin Lokacin Sallah A Zamfara

Wani ganau ya ce ’yan bindigar sun mamaye masallacin ne da misalin karfe 5 na Asuba, a lokacin da ake shirin fara salla.

Garba ya ce, “Za mu fara sallar asuba, kwatsam sai ’yan bindiga suka shigo masallaci suka umarci kowa ya fito ya bi su.

“Kowa ya yi kokarin guduwa domin tsira amma suka tare ko’ina suka gargade mu cewa za su kashe duk wanda ya yi yunkurin guduwa.


“Na samu na iya tsalle daga tagar kuma da sauri na shiga wani kango da ke kusa da masallacin na boye kaina,” in ji shi.
Shaidan ya bayyana cewa ’yan bindigar sun bar baburansu a nesa da masallacin don kada a lura da motsinsu.

Ya kara da cewa, “Daga baya sun tafi da mutanen zuwa inda baburansu suke, suka tafi da su.”

A cewarsa, adadin mutanen da aka sace a masallacin zai iya wuce 30.

Ya kara da cewa “masallacin ya cika a lokacin da suka kai hari kuma kadan ne daga cikin mu suka samu tsira.”

Daya daga cikin shugabannin yankin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce jami’an tsaro na ci gaba da bin diddigin ’yan bindigar domin kubutar da wadanda aka sacen.


Karamar hukumar Tsafe dai na daga cikin kananan hukumomin jihar da ke fama da matsalar ’yan bindiga.

Titin Tsafe zuwa Gusau ya zama wuri mafi hadari a jihar inda a kullum ake sace mutane.

A ’yan kwanakin nan an kashe ’yan bindiga da dama a karamar hukumar lokacin da wasu gungun ’yan bindiga guda biyu suka yi arangama.

(AMINIYA)

Saturday, 11 February 2023

Canjin Kudi Ya Rage Satar Mutane Da Karbar Rashawa —Malami

Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya bayyana cewa canjin kudi ta Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi ya taimaka wajen rage aikata ayyukan garkuwa da mutane.

Malami, ya bayyana haka ne cikin wata hira da ya yi da Gidan Rediyon Tarayya da ke Kaduna, inda ya ce jama’a ba sa ganin nasara da tsarin ya haifar.

Da yake bayyana hakan a ranar Juma’a, Malami ya ce: “Na fada muku maganar tana gaban kotu, ba za mu bijire wa kotu ba, za mu bi umarnin kotu amma muna da ’yancin fada wa kotu alfanun da tsarin ya haifar.

“Idan ba ku ga amfanin tsarin ba, ya kamata kuma a gefe daya ku ga alfanunsa.

“Idan wadancan gwamnonin sun bayyana wa kotu wahalar da ake sha saboda tsarin, ya kamata kuma a fahimci cewa tsarin a gefe daya yana warware wasu matsalolin.

“Na ba ku misali da matsalar tsaro; Tun bayan da aka kaddamar da wannan tsarin garkuwa da mutane ya ragu.

“Sannan ya rage yawan cin hanci da rashawa, don haka muna da ’yancin zuwa mu bayyana wa kotu amfanin da tsarin ya haifar.

“Kotun ta yanke hukunci ba tare da sauraron bangaren gwamnati ba, amma ta sanya 15 ga Fabrairu a matsayin ranar da za ta saurari tsagin gwamnati.


Kowa ya san dalilin da aka zabi Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, saboda ya yaki cin hanci da matsalar tsaro ya kuma bunkasa tattalin arziki. Don haka za mu bukaci kotu ta kalli kowane bangare.”


Idan ba a manta ba a satin da ya wuce ne gwamnatocin jihohin Kaduna, Zamfara da Kogi suka maka Gwamnatin Tarayya a Kotun Koli inda suka bukaci kotun da dakatar da hana amfani da tsofaffin takardun kudi.


Wannan dai na zuwa ne bayan wahala da talakawa suka shiga sakamakon canjin kudi da CBN ya yi, wanda hakan ya sa kasuwancin wasu ke neman durkushewa.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...