Search This Blog

Showing posts with label Hutu. Show all posts
Showing posts with label Hutu. Show all posts

Sunday, 7 April 2024

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutu

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Talata da Laraba 9 da 10 ga Afrilu, 2024 a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah.

Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar, Aishetu Ndayako ya fitar ranar Lahadi.

Ministan ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan mai alfarma.


Tunji-Ojo ya yi kira gare su da su yi koyi da kyawawan dabi’u da suka hada da kyautatawa, soyayya, hakuri, zaman lafiya, makwabtaka, tausayi, kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayar da misali da shi.
(SOLACEBASE)

Tuesday, 3 October 2023

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Hutun Bikin Takutaha

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ayyana yau Laraba 4 ga Oktoba, 2023 a matsayin ranar hutu domin tunawa da haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

A Cikin sanarwar da Kwamishinan yada labarai na Kano, Injiniya Abba Malam Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu, Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da lokutan bukukuwa domin yin tunani a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.

Ya kuma bukaci jama’a da su rika yin addu’a domin samun zaman lafiya da ci gaba a Kano a Najeriya baki daya.

Ya yi addu’ar Allah ya ganar damu wannan lokaci mai wuya, ya kuma sa mu dace a wannan damina da kuma damina mai zuwa.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...