Posts

Showing posts with the label Zargin Batanci

Zargin Batanci: Kotu Ta Ba Da Belin Dokta Idris Abdulaziz

Image
Kungiyar Fityanul Islam ta maka shi a kotu bisa zargin batannci ga Manzon Allah (SAW), zargin da malamin ya karyata. Kotu ta bayar da belin malamin Musuluncin nan, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, wanda ake zargi da batanci ga Manzon Allhah (SAW). Kungiyar Fityanul Islam ce dai ta maka malamin a kotu bisa zargin sa da kalaman batannci ga  Manzon Allah (SAW), zargin da malamin ya musanta.