Posts

Showing posts with the label Aure

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tantance Lafiya Kafin Aure A Kano

Image
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da dokar tantance lafiyar mata kafin aure a jihar Kano a hukumance, wadda ta tanadi duba lafiyar duk masu son aure. Kamar yadda sabuwar dokar ta tanada, ba za a yi aure ba a Kano ba tare da ba da takardar shaidar tantance lafiyar jinsin halitta, hepatitis B da C, HIV/AIDS, da sauran cututtuka masu alaka da su ba. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce dokar tana ganin ya zama dole domin rage yiwuwar haihuwar yara masu fama da matsalolin lafiya kamar su sickle cell anemia, HIV/AIDS, da hepatitis. Wannan shiri dai ya yi daidai da kudurin gwamnan jihar Kano na inganta da samar da yanayi mai kyau ga fannin kiwon lafiya, da nufin ganin Kano ta kubuta daga matsalolin kiwon lafiya ko kuma rage radadi. Dokar ta wajabta yin gwajin tilas na HIV/AIDS, Hepatitis, genotype, da sauran abubuwan da suka dace kafin aure. Har ila yau, ya haramta duk wani wariya ko kyama ga mutanen

Hisbah Ta Wanke Matar Da Ta Auri Saurayin ’Yarta A Kano Daga Zargi

Image
  Kwamitin da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kafa kan binciken auren matar da ta auri saurayin ’yarta, ya wanke ta daga zarge-zargen da ake mata. Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Alhaji Lawan Ibrahim ya fitar a Kano a ranar Talata. Sanarwar ta ce “Gabatar da rahoton binciken da kwamiti ya ya yi karkashin jagorancin Kwamanda Malam Hussain Ahmed, an gano auren halal ta yi kuma ta cika duk wasu sharuda da addini ya tanadar.” Sanarwar ta kuma ce bincikensu ya nuna cewar matar mijinta ya sake ta tun da fari kuma ta yi iddar wata uku kamar yadda addinin Musulunci ya tsara, kafin daga bisani ta auri saurayin ’yarta da ta daina so. Mataimakin Kwamandan ya yi watsi da zargin da ake wa matar na cewar ita ta kashe aurenta don ta auri saurayin ’yarta. “Auren halal suka yi kamar yadda Musulunci ya tsara, shi ya sa Kwamandan Hisbah a Karamar Hukumar Rano ya jagoranci daurin auren.” Babban Kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar, Harun Ibn-Sina, ya jinjina wa kwamitin kan yadda suka gudana

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero Ya yi sabon Aure

Image
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya auri mata ta biyu Hauwa'u Adamu Abdullahi Dikko a Kano ranar Juma'a. Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa an gudanar da daurin auren  ne a gidan marigayi Jarman Kano Farfesa Isah Hashim da ke unguwar Nasarawa GRA a cikin babban birnin tarayya. Sannan kuma Madakin Kano Alhaji Yusuf Nabahani Ibrahim ne ya wakilci Mai Martaba Sarkin a lokacin daurin auren, yayin da Alhaji Shehu Hashim ya kasance waliyin  amarya.

Ka da ka shekara goma da mata daya - Sheikh Daurawa

Image
Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya ce shawarci maza cewa ka da su kuskura su shekara 10 da mace daya matukar suna da burin kara aure. Sheikh Daurawa, ya bayyana haka ne a zantawarsa da gidan rediyon Freedom da ke Kano haka ne, inda ya ce idan namiji ya kai wannan shekarun da mace daya, lokaci ya kure masa. “Kada ka wuce shekara 10 idan za ka kara aure ba ka kara ba. Idan ka wuce shekara 10 akalla kana da ‘ya ‘yar shekara takwas ko tara. “Da zarar ’yarka ta kai shekara 15 ba ka kara aure ba, to wacce zaka auro da wuya ta wuce shekara 20. Za ka ga tsakaninsu da ’yarka bai wuce ’yan tazarar shekaru ba. “Saboda haka matarka ta samu abokiyar rigima. Akwai wadda za ta iya tura ’yarta ta samu amarya su rika rigima ko ta yi ta dukan amaryar saboda ta fi karfinta. “…Saboda haka wanda zai yi aure ya shirya da wuri, kuma kada duk dadin miyar mace ka ce ba za ka kara aure ba,” in ji Shehun malamin. Karin aure ko yi wa uwar gida kishiya na tayar da kura