Posts

Showing posts with the label Matsalar tsaro

Rashin tsaro: Gwamnatin Kano Tayi Alkawarin Taimakawa Gwamnatin Tarayya Akan Yaki Da Masu Ta'addanci da Satar Mutane

Image
Gwamnatin jihar Kano ta lashi takobin marawa shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na dakile illolin rashin tsaro da ke dagula zaman lafiya a kasar nan. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi wannan alkawarin ne a ranar Juma’a a lokacin da ya karbi bakuncin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Muhammad Idris a ziyarar ban girma da ya kai gidan gwamnati. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan ya ce ya dace a hada kai da gwamnatin tsakiya domin dakile wuce gona da iri domin dawo da ci gaban kasa. Alhaji Yusuf ya yabawa shugaba Tinubu bisa yadda ya yi biyayya ga kiran da ya yi na sake bude iyakokin Najeriya da wasu kasashe, matakin da zai taimaka wajen rage wahalhalun tattalin arzikin kasar. Ya kuma bayyana ziyarar a matsayin wacce ta dace da la’akari da yadda ta ke gudanar da harkokinta da masu ruwa da tsaki ciki har da ‘yan kasuwa da suka yi alkawarin yin duk abin da ya kamata na marawa gwamnatin taray

Zan Kammala Aikin Tashar Jiragen Ruwa Ta Baro Idan Kuka Zabe Ni – Atiku

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya yi alkawarin kammala aikin tashar jiragen ruwa ta Baro da ke Jihar Neja, muddin aka zabe shi a zabe mai zuwa. Atiku ya kuma ce jam’iyyarsa ce kawai take da siddabarun da za ta magance kalubalen tsaro da ya addabi kasar, musamman ma Jihar Neja. Burkina Faso ta ba sojojin Faransa wata daya su fice daga kasarta Ya yi wadannan alkawuran ne lokacin da yake jawabi ga wasu kusoshi da magoya bayan jam’iyyar a Minna, babban birnin Jihar Neja ranar Asabar. Atiku ya ce PDP ce ta faro aikin na Baro rimi-rimi lokacin da take mulki, amma APC na zuwa ta yi watsi da shi. A cewar tsohon Mataimakin Shugaban Kasar, “Muna addu’ar Allah Ya kawo zaman lafiya a Jihar nan. Kun san PDP ce kawai za ta iya dawo da zaman lafiya a Neja. Lokacin da take mulki daga 1999 zuwa 2015, akwai matsalar tsaro a Neja? Muna so mu tabbatar muku cewa muddin PDP ta dawo, matsalar za ta zama tarihi. “Muna kuma so mu tabbatar muku cewa aikin tashar Ba