Posts

Showing posts with the label Ogun

Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Bukatar INEC Da Gwamnan Ogun A Shari’ar Zabe

Image
Kotun koli ta karbi karar da Jam’iyyar PDP da dan takararta a zaben gwamnan Ogun, Ladi Adebutu, suka daukaka domin kalubalan ar nasarar Gwamna Dapo Abiodun. Kwamitin alkalai biyar na ko tun,  karkashin jagorancin Mai Shari’a Inyang Okoro  ya  kuma ki sauraron karan da Jam’iyyar APC ta Gwamna Dapo Abiodun da Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) suka daukaka daga bisani a kan lamarin. A  yayin zaman na  ranar Alhamis, kwamitin alkalan ya sanar da lauyan APC, Wole Olanipekun (SAN) cewa babban karar da aka daukaka a gaban ko t un  koli ya hade buka t arsu . Adebutu da PDP suna neman Ko tun Koli t a kwace kujerar Gwamna Abiodun, a bisa dalilin saba dokar zabe, magudi da kuma rashin cancantarsa. Kotun Koli za ta yanke hukunci kan Zaben Gwamnan Filato ranar Juma’a An kashe mai unguwa an yi wa mai gadi yankan rago a Katsina Da yake gabatar da jawabinsa, lauyan Adebutu da PDP, Chris Uche (SAN) ya ce ya kamata INEC ta sake gudanar da zabe a rumfunan zabe 99 da aka soke zabensu. PDP da Adebutu suna kuma s