Search This Blog

Showing posts with label Muhammadu Buhari. Show all posts
Showing posts with label Muhammadu Buhari. Show all posts

Monday, 14 July 2025

NAHCON Ta Yi Jimamin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ƙarƙashin jagorancina, Farfesa Abdullahi Sale Usman, ta bi sahun sauran al’ummar Najeriya wajen jimamin rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.

 

Wannan rashin ya zo ne a daidai lokacin da ƙasa ke cikin alhini na rashin wani fitaccen attajiri kuma mai jinƙai, Alhaji Aminu Dantata. 


Wannan al’amari wani tunatarwa ne gare mu duka kan cewa kowa yana da lokacin tafiyarsa, kuma yana ƙara bayyana wa matasa bukatar shiryawa don karɓar ragamar shugabanci na gaba da gina rayuwa bisa gaskiya, amana, hangen nesa da kyakkyawar manufa ga makomar Najeriya.

 

Dukkan su biyu, kowannensu da irin nasa salo, sun kasance tamkar madubin darussa da matasa za su duba su dauki darasi domin gina ingantacciyar ƙasa. Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari ya shahara wajen tsantsar gaskiya, rikon amana da ladabi – wanda ya sanya ya zama abin ƙauna da koyi ga talakawa da dama.

 

Haka kuma, Alhaji Aminu Dantata ya shahara da hikimar kasuwanci da arziki wanda ya ke amfani da su wajen tallafawa ayyukan jinƙai da ci gaban al’umma. Ya gada kasuwanci daga mahaifinsa kuma ya gina bisa wannan harsashi, har ya bunƙasa sha’anin kasuwancin iyalansu da bayar da gudunmawa wajen ci gaban tattalin arziki da zamantakewar Najeriya.

 

Za a ci gaba da tuna da su bisa wasu manyan abubuwan alheri da suka aikata waɗanda ba za a iya ƙididdigewa ba da kuma gudunmawar da suka bayar wajen gina ƙasar nan.

 

Rasuwarsu a lokaci guda babban rashi ne ga ƙasa, amma kuma wani darasi ne ga matasan da ke tasowa a yau wajen tabbatar da ƙimomin da ke kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba mai ɗorewa.

 

Allah ya gafarta musu, ya sanya su cikin Aljannatul Firdaus, ya ƙarfafa danginsu da daukacin al’ummar Najeriya a wannan lokaci na jimami.

Wednesday, 20 December 2023

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura

Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000)

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su. 

Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen Daura murna, bisa ga Jajirtaccen Shugaba da suka samu.

Taron ya samu Halartar Tsohon Shugaban Ƙasar Nigeria, Gen. Muhammadu Buhari, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa PhD, Shugaban Jam'iyyar APC na Jiha da Mataimakinsa, Yan Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, kwamishinoni da masu bada shawara, Wakilin Mai Martaba Sarkin Daura, Hajia Ambarud Sani Wali, Shugaban karamar hukuma, Tsofaffin yan Majalissar Jiha, Barr. Ahmad Usman El-Marzuq, da sauran manyan baƙi

Kakakin Majalissa ya bayar da kyautar Sa (Bijimi) ga Muhammadu Buhari, da kyautar Doki ga Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa. 
 
Sannan Ƙungiyoyin Daura Forum, DECA, DEDA, Health and Education Department, Ƙungiyoyin Addini, da Babbar Ƙungiyar, Daura Consortium sun bayar da Lambobin Yabo da Girmamawa (Award) ga Mai Girma Kakakin Majalissar Dokoki a bisa ayyukan Alkhairin da yake aikatawa ba dare ba rana a Daura

Haka zalika Ƙungiyar Daura Forum ta bada lambar yabon ga  Muhammadu Buhari, da Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa  

Daga karshe Kakakin Majalissa yayi Godiya ga manyan baƙi da suka halarci wannan Babban taron, sannan yayi Addu'a da fatan Allah ya maida kowa gidanshi lafiya, l

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...