Posts

Showing posts with the label Muhammadu Buhari

NAHCON Ta Yi Jimamin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Image
Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ƙarƙashin jagorancina, Farfesa Abdullahi Sale Usman, ta bi sahun sauran al’ummar Najeriya wajen jimamin rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.   Wannan rashin ya zo ne a daidai lokacin da ƙasa ke cikin alhini na rashin wani fitaccen attajiri kuma mai jinƙai, Alhaji Aminu Dantata.  Wannan al’amari wani tunatarwa ne gare mu duka kan cewa kowa yana da lokacin tafiyarsa, kuma yana ƙara bayyana wa matasa bukatar shiryawa don karɓar ragamar shugabanci na gaba da gina rayuwa bisa gaskiya, amana, hangen nesa da kyakkyawar manufa ga makomar Najeriya.   Dukkan su biyu, kowannensu da irin nasa salo, sun kasance tamkar madubin darussa da matasa za su duba su dauki darasi domin gina ingantacciyar ƙasa. Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari ya shahara wajen tsantsar gaskiya, rikon amana da ladabi – wanda ya sanya ya zama abin ƙauna da koyi ga talakawa da dama.   Haka kuma, Alhaji Aminu Dantata ya shahara da hikimar kasuwanci da arziki wa...

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Image
Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000) Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su.  Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen D...