Search This Blog

Showing posts with label Dr Dukawa. Show all posts
Showing posts with label Dr Dukawa. Show all posts

Tuesday, 9 May 2023

Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na 3 - Dr Dukawa


HALIN DA WASU TASHOSHIN MOTA SUKE CIKI 

A bisa kiyasi, tashar Na’ibawa a Kano ba za ta gaza shekara arba’in (40) ba. Saboda an samar da ita ne a zamanin marigayi gwamnan tsohuwar jihar Kano Alhaji Abubakar Rimi (1979 – 1983). Amman har izuwa yau tashar tananan jiya ya yau: kango wanda babu wani abu da yake nuna ana samun kudi a wurin; babu kwalta, babu interlocks, babu dabe kowane iri! Zaiyar kasa. Sai yalwar leda da sauran nau’i na shara. Babu wani lafiyayyen makewayi. Da na bukaci wurin yin bawali sai aka nuna min wani uban juji a yammacin cikin tashar. Sai da roki wani dan bola jari cewar ya dan kauce zan kama ruwa. 

Na tabbatar idan ruwa ya sauka mummunan halin da tashar ke ciki ba zai gaza na tashar Unguwa Uku ta Kano ba, wacce na yi rubutu akan nata halin da take ciki a sherarar 2020. 

An yayyanka pilotai a cikin tashar Na’ibawa. Wasu an gina shaguna ana gudanar da ciniki wasu kuma an saka fandisho na gini ba a yi ginin ba. Babu Masallaci sai ‘yar musalla amman har da lasifika. Ko yaya aka yi a kasar Musulmi irin Kano za a yi tashar mota ta shekara arba’in ba a samar da masallaci ba sai abin ya daurewa mutum kai. Alhali ya kamata ace izuwa yanzu har dakin shan magani, da karamin dakin ATM da ofishin aika sako (akwatin gidan waya) na gaggawa, da kuma ofishin ‘yansanda ya kamata ace an samu.

Halin da na samu tashar mota a Yola da Jalingo bai sha banban da yadda na baro a Kano ba. Babu wani abu na cigaba. Sai turbaya da shara da bola.
Anan zan nanata kirana ga kananan hukumomi (LGAs) a Arewacin Najeriya cewar su tuna amanar da suka dauka na gudanar da ayyukan da aka zayyana a makale na hudu (fourth schedule) na Tsarin Mulkin Najajeriya. Daga ayyukansu akwai samarwa da kula da tashoshin mota. Wannan ba ya nufin a shata kango motoci su rika shiga suna lodi ‘yan rabanu (masu karbar kudin shiga) kuma suna karbar haraji kawai ba. 

Amman yana nufin a inganta tashoshi ta hanyar samar da yanayi mai kyau da tsabta da tsaro. Kunyoyin da suke karbar nasu kason a wurin direbobi su ma su sani cewar babban aikinsu shine su inganta sana’ar ta hanyar bibiyar hukumomi da neman su sauke nauyinsu da kuma taya hukumomin samar da wasu abubuwan inganta rayuwa a wurin sana’a. sabanin haka za su rika cin haram ne na wannan kudaden da suke karba.

Monday, 8 May 2023

Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na Biyu


 


Daga Dr Sa'idu Ahmad Dukawa

TSARIN DAUKAR FASINJA A TASHA

Bayan da na yi tambayi game da tsarin daukar fasinja a tashar mota, na sami bayanin cewa mutum zai iya zuwa tsahar Na’ibawa (wacce a yanzu aka sakawa suna “tashar Kano Line”) ya yi booking (biyan kudi kafin ranar tafiya). Don haka sai na je ofishin Adamawa Sunshine (wanda alal hakika shago ne a cikin tashar da dan teburi da mutumin da yake karbar kudi ya rubuta rasiti), na biya kudina ana kashegarin ranar tafiya.

Na tambaya mutum nawa ake dauka a mota kirar sienna? Aka ce min ana daukar mutum takwas ne, fasinja biyu a gaba, uku a tsakiya, uku a karshe. Amman fa Bature ya yi motar ne domin daukar fasinja biyar: guda a gaba, biyu a tsakiya, biyu a karshe. Don haka ana wuce kima (overload) na mutum uku. A motar ‘yankasuwa kuwa har mutum hudu ake sakawa a tsakiya, kamar yadda na ganewa idona a yayin dawowata daga Jalingo zuwa Kano. Allah ya kiyaye, a duk lokacin da aka gamu da hadari, za ta yiwu a yi asarar rayuka tara zuwa goma a cikin mota guda. A inda aka san kimar rai, duk yadda za a yi a rage asarar rai guda ana yi.

Ko me yasa dole sai an yi overload a motocin haya a Najeriya? Dalilan sanannu ne. farko dai akwai tsadar man fetur. Na biyu akwai biyan haraji hawan hawa, hukuma ta karba, kungiyoyi su amsa, yan kamasho su yaga, a dankawa ‘yan wururu masu taro fasinja daga hanya su kawo shi gindin mota, a dankawa masu gadin tasha, a yi ta mikawa jami’an tsaro kashi kashi (na kidaya shingen jami’an tsaro kimanin dozen guda a tsaknin Jalingo da Gombe kadai). Ga kuma tsadar kayan mota (spare parts) tunda kusan komai sai an yi odarshi, ba a kera komai a kasar. Ga mamallakin mota yana so ya mayar da kudinsa da wuri, don haka yana son a rika kawo balance mai tsoka a duk rana.

A karshe ga bukatar Direban motar na ya samu abinda zai shiga gida da shi ya sallami iyali. Idan aka hada duk wadannan bukatun akan fasinja kuma ba zai iya dauka ba. Don haka akan dole ake gwammacewa a cunkusa fasinja, wani a jikin wani, kamar kifin sardine.

Akwai kuma abinda yake ya shafi dabi’a ta rashin tsari da ci da zuci da rashin ganin kimar dan Adam wacce take tattare da mutane da yawa, barin idan sun san babu wata doka za ta hau kansu. Alal misali, na biya kudin kujera uku na tsakiya yayin da zan tafi, saboda tare da iyali zan yi tafiyar.

Amman ko da muka zo tasha sai muka taras an cushe wurin ajiyar kaya, babu inda zamu saka ‘yan kananan jakunkunanmu kwara biyu, wadanda idan mun yi tafiya a jirgin sama ba ma auna su, da su muke shiga jirgi, saboda karancin girma ko nauyi da suke da shi. Sai aka nemi wai tunda mu biyu ne kacal a tsakiya, wurin zai ishemu har kayanmu. Ni kuma nace ban amince ba. Daga dukkan alamu kuma sun riga sun sayar da wurin ajiyar kayana, sun karbi sakon kaya wanda shima na samu labarin kudin kujera ake biyansu. Na duba rasitin da aka bani ko akwai lambar wayar ofis sai na kai korafi sai naga in banda sunan na “Adamawa Sunshine” babu komai a jiki, babu lambar waya, babu adireshi! A karshe dai sai saukemu aka yi daga motar, ni da iyalina, na jira wata ta yi lodi bayan sa’a uku, sannan muka kama hanya.

A nan akwai bukatar ace daga cikin jerin masu karbar kudin shiga akwai wadanda suke sa ido wajen ganin an bi ka’ida, an cika alkawari, ko Allah ya sa albarka a harkar da kuma a rayuwarmu baki daya. Wasu shawarwarin da za su biyo baya da za su karfafi wannan, da yardar Allah.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...