Posts

Showing posts with the label Monday Market

Buhari Ya Je Maiduguri Domin Jajantawa 'Yan Kasuwar Monday Market

Image
Shugaban Kasa Muhamamdu Buhari ya isa Jihar Borno, domin jajanta wa ’yan kasuwar da iftila’in gobora ta shafa a Kasuwar Monday da ke Maiduguri. An wayi gari ranar Lahadi a Maiduguri da gobarar, wadda ta lakume dubban shaguna a kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Jihar Borno da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya. ’Yan sanda na ci gaba da tsare Ali Madaki kan daukar bindiga a yakin neman zabe Ana sa ran a yayin ziyarar ta ranar Alhamis, Buhari zai je Fadar Shehun Borno, inda zai jajanta wa ’yan kasuwar da suka yi asarar dukiyoyinsu a gobarar ta ranar Lahadi. Shugaban kasar zai kuma kaddamar wa wasu ayyuka da suka hada da rukunin gidajen da Gwamna Babagana Zulum ya gina da wasu tituna a garin Maiduguri. Sauran su ne Cibiyar Kula da Masu Cutar Kansa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da kuma Tashar Iskar Gas ta kamfanin NNPC.