Posts

Showing posts with the label Abduljabbar Umar

Sabon Kwamishinan Kasa Na Kano Ya Kama Aikinsa

Image
Sabon kwamishinan ma’aikatar kasa da tsare-tsare ta jihar Kano, Alhaji Abduljabbar Umar Garko ya fara aiki tare da alkawarin daukar kowa da kowa. A Sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na ma'aikatar Murtala Shehu Umar ya sanyawa hannu,  yace Abduljabbar Garko ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga ma’aikatan ma’aikatar a dakin taro na ma’aikatar bayan zagaya ofisoshin da misalin karfe 8:00 na safe. Kwamishinan ya bayyana ma’aikata a matsayin abokan hadin gwiwa da ake ci gaba da yi inda ya bukace su da su bayar da cikakken goyon baya da hadin kai ga wannan gwamnati ta Alhaji Abba Kabir Yusuf a kokarinta na farfado da harkokin kula filaye a jihar. “Muna kan mulki ba yakin neman zabe ba ne, don haka ya zama dole mu samar da ayyuka masu inganci da shugabanci nagari ga daukacin ‘yan jihar Kano, kuma za mu cimma hakan ta hanyar ba da goyon baya da hadin kai.” Inji Garko. "A matsayina na kwamishina a wannan ma'aikatar, zan ba ka damar gudanar da ayyuka