Posts

Showing posts with the label Likitoci

Likitocin Najeriya Sun Fara Gudanar Da Yajin Aikin Gama-Gari

Image
Likitoci Masu Neman Kwarewa a fadin Najeriya sun fara yajin aikin sai abin da hali ya yi daga safiyar nan ta Laraba. Kungiyar likitocin (NARD) ta sanar da shiga yajin aikin ne jim kadan bayan zaman Majalisar Zartarwarta da ya gudana a Legas a ranar Talata. Shugaban kungiyar, Dokta Orji Emeka Innocent, ya dora laifin shigarsu yajin aikin a kan jan kafar Gwamnatin Tarayya wajen biyan bukatunsu da suka jima da gabatar mata. Dokta Orji ya ce sai da kungiyar ta kara wa’adin da suka ba gwamnati da mako biyu domin ta biya bukatun nasu, amma duk da haka, sai da ta kai ga sun yi yajin aikin gargadi na kwana biyar daga ranar 17 zuwa 21 ga watan Yuli da muke ciki, kuma har yanzu gwamnatin ta ki yin abin da ya kamata. Ya kara da cewa kafin a kai ga haka, sai da aka shafe sama da mako bakwai ba tare da gwamnati ta aiwatar da yarjejeniyoyin da bangarorin suka kulla a zaman sulhun da ministan kwadago ya jagoranta ba, duk kuwa da cewa an sanya wa’adin aiwatar da su  Bukatun likitocin sun h

Yajin aikin likitocin Najeriya ya jefa majinyata a halin kunci

Image
Tarin asibitoci a sassan Najeriya sun fada halin garari saboda karancin likitocin da ke duba marasa lafiya sakamakon yajin aikin gargadin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta NARD ke yi kasar, inda bayanai ke nuna cewa tuni majinyatan da ke bukatar kulawar gaggawa suka sauya akalar duba lafiyarsu zuwa asibitoci masu zaman kansu sakamakon cunkoson da ake gani a asibitocin gwamnati. A larabar da ta gabata ne mambobin kungiyar ta NARD suka tsunduma yajin aikin a wani yunkuri na nuna bacin ransu game da rashin cika musu alkawuran da ke tsakaninsu da gwamnati ciki har da karin albashi da akalla kasha 200. Sai kuma yunkurinsu na kalubalantar kudirin dokar da ke gaban Majalisar kasar da ke shirin kange daga fita ketare don yin aiki har sai bayan sun yi aikin shekaru 5 a cikin Najeriya. Haka zalika kungiyar likitocin na bukatar gwamnatin Najeriyar ta biya mambobinta bashin kudaden albashin da suke binta tun shekarar 2015 baya daukar tarin ma’aikatan bangaren lafiya saboda kar