Search This Blog

Showing posts with label Sulhu. Show all posts
Showing posts with label Sulhu. Show all posts

Tuesday, 28 November 2023

Abin Da Ya Kawo Cikas A Sulhun ECOWAS Da Sojin Nijar — Yusuf Tuggar

Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce sun yi tayin tattaunawa domin kawo ƙarshen tankiyar da ke tsakanin Ƙungiyar Raya Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da sojojin da suka kifar da Shugaban Nijar Mohammed Bazoum, amma hakan bai yiwu ba, don kuwa shugabannin sojojin sun ƙi amincewa da yunƙurin.

Ambasada Tuggar ya faɗi hakan ne a wata hirarsa da BBC, yana mai cewa duk wata magana da ta shafi a saki Shugaba Bazoum, sojin ba su amince da ita ba.

’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 2 a Imo
Abdul Amart ya siya wa iyalan Aminu S. Bono gida
“Sun ce kar ma a yi wannan maganar, kar ma a sa shi cikin sharuɗɗan yin sulhu,” in ji Yusuf Tuggar.

Ya bayyana cewa babu ta yadda za a iya samun sulhu a wannan yanayi.

“Za su ci gaba da rike shi kenan ya yi zaman dindindin a kulle?”


Ministan ya ce sojojin da suka yi juyin mulki ne suka janyo wa Nijar takunkumin da ECOWAS ta ƙaƙaba mata, da kuma shiga halin da take ciki.

Ya ce abin da suke buƙata shi ne a saki Shugaba Bazoum.

“Muna son sojojin su saki Bazoum ya fita, a kai shi wata ƙasa daban. Ba maganar dawo da shi kan mulki ake yi ba,” in ji ministan.


Ya ƙara da cewa, duk wani yunƙuri da suka yi, sojojin sun ƙi ba da haɗin-kai ta kowanne yanayi, inda suka ce ba sa son a yi maganar ma kwata-kwata.

“Ta yaya za a yi sulhu a haka, mene ne sojojin za su yi saboda in ana son yin sulhu tsakanin mutane, gefe ɗaya zai ce ya haƙura da abu kaza, ɗaya gefen ma ya ce haka.

“To su kwata-kwata cewa suka yi, sai dai a yi musu abin da suke so,” in ji Tuggar.

Ya ce ECOWAS ba ta da matsala da ƴan Nijar kuma ba ta jin daɗin halin da suke ciki.

Ya ƙara da cewa matsalarsu ita ce sojojin da suka kama Shugaba Bazoum suka riƙe, duk da yake suna ganin akwai hanya mai sauƙi ta warware rikicin.

Ministan harkokin wajen Najeriyar ya ce dole ne idan mutane suka yi ba daidai ba a tsawatar musu.

A cewarsa, sojojin ma ba yadda suka iya da junansu don kuwa, kowa na ƙoƙarin samun ƙarfin iko a Nijar, inda a gefe guda suka bar ƴan ta’adda na can suna cin karensu babu babbaka.

Watanni huɗu bayan kakaba wa jamhuriyar Nijar takunkumi da ƙungiyar ECOWAS ta yi, sakamakon juyin mulkin sojoji, har yanzu ƴan ƙasar na ci gaba da ɗanɗana kuɗa da rayuwar ƙunci.

Farashin kayan masarufi ya yi tashin gwauron zabi, saboda rufe iyakar ƙasar da Najeriya ta yi, da kuma yanke hulɗar kasuwanci da ƙasashen ECOWAS suka yi da Nijar.

(AMINIYA)

Tuesday, 31 January 2023

Muna Kan Tataunawa Da Kwankwaso Da Obi - Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Dala LGA Donates Building as Operational Base to Multi-Joint Task Force

In a show of unified resolve against drug abuse and related crimes, Dala Local Government has donated a local government–owned b...