Posts

Showing posts with the label Zaben shugaban Najeriya na 2023

Ana ɓarnata kuɗin gwamnati a Majalisar Dokokin Tarayya - Shekarau

Image
  A Najeriya, tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon ɗan majalisar dattijan ƙasar, Ibrahim Shekarau ya ce kasar ba ta bukatar majalisar dattawa da ta wakilai, kasancewar aiki iri ɗaya suke yi. A nasa ra'ayin, ɓata kudi ne kawai gwamnati ke yi wajen tafiyar da majalisun biyu. Najeriya na da zauruka biyu na majalisar dokokin tarayya, wadda ta haɗa da Majalisar Dattaijai mai wakilai 109. Sai kuma Majalisar Wakilan Tarayya, wadda take da wakilai 360. A tattaunawarsa da BBC, Shekarau ya ce kamata ya yi Najeriya ta rungumi tsarin mulki irin na Birtaniya, wanda aikin ƴan majalisar bai wuce na wucin-gadi ba. Sai dai Shekarau ya ce gyara irin tsarin na majalisar dokoki a Najeriya abu ne mai matuƙar wahala domin sai an yi gyara a kundin tsarin mulkin ƙasar. Kuma cewarsa, akwai yiwuwar ƴan majalisar dokokin, waɗanda dole ne sai an samu amincewarsu kafin a iya sauya dokar, ba za su goyi bayan canza ta ba. Sanata Shekarau ya ce “kowane daga cikin ƴan majalisar tarayya 469, an ba shi dama ya ɗauk

Ganawar da ‘yan majalisar wakilan jam’iyyun adawa suka yi a Najeriya sun yi azarɓaɓi - Masana

Image
  Masu sharhi kan harkokin siyasa a Najeriya na ci gaba da tsokaci a kan ganawar da ‘yan majalisar wakilan da suka fito daga bangaren jam’iyyun hamayya suka yi a makon nan. Ganawar dai ta samu halartar sabbin ‘yan majalisun da kuma wadanda aka sake zaba domin wakiltar jama’arsu a majalisa ta 10 da ake shirin kafawa a watan Yunin 2023. Farfesa Kamilu Sani Fagge, malami ne a tsangayar siyasa a Jami’ar Bayero ta Kano, ya shaida wa BBC cewa, irin wannan ganawa rikita-rikitar siya ce kawai. Ya ce: “ A gaskiya sun yi sauri wajen gudanar da wannan taro, to amma ina ga sun yi kokari ne da ake cewa a tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro domin idan an zo an rantsar da majalisar, kuma ba su yi wani abu da zai kawo rudani ba, to ko shakka babu ba za a yi da su a majalisar ba.” Ya ce, ya kamata ‘yan majalisar da suka yi wannan taro su sani cewa har yanzu fa akwai sauran zaben ‘yan majalisun da ba a kammala su ba. Malamin ya ce: “ A ka’idar zabe na majalisar wakilai kafin a ce jam’iyya na da rinjaye, d

Yadda masu son muƙamin shugaban majalisa ke sayen ƙuri'un sanatoci - Ndume

Image
  A Najeriya bayan kammala zaɓukan ƙasar a yanzu hankali ya karkata kan shugabancin zaurukan majalisun dokoki. Tuni dai wasu 'yan majalisun da ke son ɗarewa kujerun shugabancin majalisun suka fara bayyana sha'awarsu ta hanyar kamun ƙafa a wajen masu ruwa da tsaki na jam'iyyunsu da kuma zaɓaɓɓun 'yan majalisar. Sai a watan Yuni mai zuwa ne za a ƙaddamar da majalisar dokokin ta goma, daga nan kuma a fara shirye-shiryen zaɓen shugabannin majalisun. To sai dai wasu 'yan majalisun sun fara zargin cewa ana amfani da kuɗi wajen sayen bakin 'yan majalisun domin zaɓen wasu a matsayin shugabannin majalisun. Sanata Ali Ndume ɗan majalisar dattawa ne daga jihar Borno ya kuma shaida wa BBC cewa akwai zargin da ake yi na cewa wasu na amfani da kuɗi wajen ganin sun samu ɗarewar kujerar shugaban majalisar dattawa. Ya ce a yanzu siyasar ƙasar masu hannu da shuni, ko masu kuɗi su ne ke juya ɓangaren siyasar ƙasar. ''Dandalin siyasarmu ya cika da irin waɗannan mutanen da s