Search This Blog

Showing posts with label Biliyan biyar. Show all posts
Showing posts with label Biliyan biyar. Show all posts

Thursday, 2 November 2023

Majalisa Ta Yi Fatali Da Bukatar Tinubu Ta Kashe Biliyan 5 Wajen Sayen Jirgin Ruwa

Majalisar Wakilai a ranar Alhamis ta yi fatali da bukatar Shugaban Kasa Bola Tinubu ta kashe Naira biliyan 5 daga cikin kwarya-kwaryar kasafin kudin tiriliyan 2.17 wajen sayen jirgin ruwa.

A maimakon haka, majalisar ta bukaci a mayar da kudin wajen kara yawan kuɗin da aka ware domin ba dalibai rancen, wanda a baya aka ware wa biliyan 10.

‘Barayin’ da suka je fashi sun ɓige da satar tukwanen miya da abinci a Kalaba
Majalisa ta amince da kwarya-kwaryar kasafin kudin Tinubu na tiriliyan 2.17
Aminiya ta rawaito cewa matakin ’yan majalisar ba zai rasa nasaba da koke-koken da ’yan Najeriya suka rika yi ba tun bayan bullar labarin, inda suka ce ya zo a daidai lokacin da ’yan kasa ke korafin kuncin rayuwa.

Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Abubakar Kabir (APC, Kano) ne ya bayyana hakan lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi jim kadan da kammala amincewa da kasafin a Abuja.

Ya ce daukar matakin ya zama wajibi la’akari da kudin da aka ware wa daliban a cikin kasafin ya yi kadan.

Abubakar ya kuma ce kwamitin ya kason da aka ware wa Ma’aikatar Tsaro daga Naira biliyan 476 zuwa 546 sakamakon ƙaruwar kalubalen tsaro.

Shugaban kwamitin ya kuma ce sun duba tare da amincewa da batun kara mafi ƙarancin albashin ma’aikata domin mika shi ga bangaren zartarwa.

Sai dai ya ce za su tabbatar suna sanya idanu ga bangaren zartarwa domin ganin sun yi abin da ya dace.

Amma daga bisani Fadar Shugaban Kasa ta ce jirgin ruwa ba na amfanin Tinubu ba ne, na Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ne
(AMINIYA)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...