Posts

Showing posts with the label Sudan

Abin Da Ya Haddasa Yakin Sudan Jamhuriyar Musulunci (Kashi Na Biyu)

Image
Datti Assalafiy✍️ Mutane biyu ne sukayi sanadiyyar yakin da ya barke a Kasar Sudan, kuma Musulmai ne abokan juna na kut da kut. Na farko sunansa: General Abdel Fattah al-Burha, shine Shugaban Sojojin Sudan wanda ya jagoranci kifar da mulkin tsohon shugaba Umar Al-Bashir ya haye kujeran mulki Na biyu sunansa: Janar Muhammad Hamdan Dagalo (Hemetti), shine mataimakin Shugaban Kasar Sudan, kuma shine babban Kwamandan rundinar tsaro na agajin gaggawa da ake kira Rapid Support Forces (RSF) Wanene Dagalo?  Kamar yadda na fada a sama, yanzu haka Dagalo shine mataimakin Shugaban Kasar Sudan, kuma shine Babban Kwamandan RSF, wato yana rike da matsayi guda biyu a Sudan kenan  Rapid Support Forces (RSF) rundinace ta tsaro da aka kafata tun a lokacin yakin basasar da akayi a yankin Dafur na Kasar Sudan, suna aiki da sarrafa makaman yaki kamar sojoji Janar Muhammad Hamdan Dagalo gawurtaccen dan ta'adda ne, kuma dan tawaye, a lokaci guda kuma dan siyasa, kamar dai misali da a nan Nige

Abun Da Ya Haddasa Yakin Sudan Jamhuriyar Musulunci (Kashi na daya) - Datti Assalafiy

Image
Datti Assalafiy✍️ Shimfida: Akwai taba addini a yakin Sudan, saboda shi tsohon shugaban Kasar Sudan Umar Albashir wanda aka masa tawaye aka hambarar dashi da karfin tsiya ya bawa Musulunci kariya sosai a Sudan, yana bawa Musulunci kariya a Sudan wanda ko Saudiyyah bata yin irinsa a Kasarta Yana daya daga cikin shugabannin Kasashen Musulunci a duniya wanda idan makiya Musulunci suka taba addinin Allah da Musulmai yake fitowa yayi magana, Kasar Iran daular masu bin addinin shi'ah sun taba yin mummunan batanci ga Sahabban Annabi (SAW) guda biyu Abubakar da Umar, a ranar ya kori Ambasadar Kasar Iran, kuma yasa aka rushe embassy na Iran dake Sudan, aka gina Sabon Masallaci a gurin, aka sanya wa Masallacin sunan Abubakar da Umar wato sunan Sahabban Annabi (SAW) Lokacin Shugaba Umar Albashir babu gidan sayar da giya a Sudan, babu gidan karuwai a Sudan, babu gidan caca da sauran guraren sabon Allah, mata basa shiga harkokin shugabanci, to wannan kariyar da ya bawa Musulunci,

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta

Image
Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta. Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan. Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta. Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar. Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gi

Air Peace Zai Kwaso Daliban Najeriya Da Suka Makale A Sudan Kyauta

Image
  Kamfanin jiragen sama na Air Peace ya ce zai kwaso daliban Najeriya da suka makale a kasar Sudan inda yaki ya barke, kyauta zuwa gida. Rikicin shugabanci ya kazance a Sudan a baya-bayan nan, har ta kai ga rufe sararin samaniyar kasar. Akalla daliban Najeriya 5,000 da ke Sudan sun nuna matukar bukatar a dawo da su gida, inda wasu daga cikinsu ke kokarin tsallaka iyaka zuwa kasar Habasha, mai makwabtaka da Sudan. Shugaban kamfanin Ake Peace, llen Onyema, ya sanar da cewa idan ’yan Najeriya da ke Sudan za su iya tsallaka iyaka zuwa kasashen makwabtakan Sudan, to kamfaninsa zai kwaso su zuwa gida a kyauta. Ya ce aikin kwaso su ya wuce a bar wa gwamnati ita kadai, saboda bai kamata a yi asarar dan Najeriya ko daya ba a rikicin na Sudan. Gwamnatin Tarayya dai ta yi alkawarin ranar Talata za ta fara kwaso ’yan Najeriyan ta kasar Habasha. Wata sanarwa da Fadar Shugaban Kasa ta fitar ta ce Ma’aikatarta Harkokin Kasashen Waje na aiki da gwamantin kasar Habasha, domin amfani da sara

Sojojinmu ne ke iko da muhimman wurare - shugaban Sudan

Image
  Janar Abdel Fattah al-Burhan, jagoran Sudan kuma babban hafsan hafsoshin sojin Æ™asar ya musanta iÆ™irarin rundunar jami'ai masu kayan sarki ta RSF, cewa dakarunta ne ke iko da fadar shugaban Æ™asa da hedkwatar sojoji da kuma filin jirgin sama. A wani saÆ™on waya da aka naÉ—a lokacin hira da gidan talbijin na Al Jazeera, Janar al-Burhan ya dage kan cewa dakarunsa ne har yanzu ke da iko. Ana ci gaba da samun rahotanni masu cin karo da juna game da abin da ke faruwa a tsawon wannan rana kan taÆ™amaimai wane ne ke iko da muhimman wurare a birnin Khartoum. BBC