Search This Blog

Showing posts with label Sudan. Show all posts
Showing posts with label Sudan. Show all posts

Tuesday, 9 May 2023

Abin Da Ya Haddasa Yakin Sudan Jamhuriyar Musulunci (Kashi Na Biyu)



Datti Assalafiy✍️

Mutane biyu ne sukayi sanadiyyar yakin da ya barke a Kasar Sudan, kuma Musulmai ne abokan juna na kut da kut.

Na farko sunansa:
General Abdel Fattah al-Burha, shine Shugaban Sojojin Sudan wanda ya jagoranci kifar da mulkin tsohon shugaba Umar Al-Bashir ya haye kujeran mulki

Na biyu sunansa:
Janar Muhammad Hamdan Dagalo (Hemetti), shine mataimakin Shugaban Kasar Sudan, kuma shine babban Kwamandan rundinar tsaro na agajin gaggawa da ake kira Rapid Support Forces (RSF)

Wanene Dagalo? 
Kamar yadda na fada a sama, yanzu haka Dagalo shine mataimakin Shugaban Kasar Sudan, kuma shine Babban Kwamandan RSF, wato yana rike da matsayi guda biyu a Sudan kenan 

Rapid Support Forces (RSF) rundinace ta tsaro da aka kafata tun a lokacin yakin basasar da akayi a yankin Dafur na Kasar Sudan, suna aiki da sarrafa makaman yaki kamar sojoji

Janar Muhammad Hamdan Dagalo gawurtaccen dan ta'adda ne, kuma dan tawaye, a lokaci guda kuma dan siyasa, kamar dai misali da a nan Nigeria mu ce Bello Turji, sannan kazamin mai kudi ne na fitar hankali, bincikena ya nuna min cewa a Sudan babu wanda ya kai Dagalo arziki, shine shugaban masu satar zinare na Kasar Sudan, kusan shine yake juya akalar hako zinare na Kasar Sudan, yayi karfin da a Sudan babu wanda ya isa ya nuna masa yatsa tun daga kan shugaban Kasa

Saboda ku tabbatar da kudinsa, lokacin da Amerika tasa aka yiwa Shugaba Umar Al-bashir zanga-zanga da tawaye, anyi wata uku a jere babu albashi a Sudan, Dagalo ne ya ara wa Gwamnatin sudan kudi aka biya albashi a fadin Kasar, yana da mayakansa na RSF sama ds guda dubu dari don har sun fi sojojin Kasar yawa,, makamin da yake hannunsu yafi na sojojin Sudan aminci

To lokacin da aka fara zanga-zangar da ta kai ga kifar da shugaba Al-bashir, kafin Sojoji su hadu da RSF su hambarar da Al-bashir, shugaba Al-bashir sai yayi wata dabara na siyasa don ya kara karfi, sai ya kira Dagalo ya bashi jagorancin rundinar  RSF, amma haka Dagalo ya zagaya ya hada kai da abokinsa shugaban Sojojin Sudan Janar al-Burhan suka kifar da Gwamnatin Al-bashir, to daga nan ne sai rundinar sojin Sudan da tayi juyin mulki ta bawa Dagalo matsayin mataimakin Shugaban Kasa, saboda suna tsoron zai iya musu juyin mulki suma, domin ya fisu karfi ya fisu kudi

Abinda ya haddasa yakin Sudan:
A cikin azumin watan Ramadan da ya gabata, Shugaban mulkin Soji na Kasar Sudan Janar al-Burhan ya kira abokinsa kuma mataimakin Shugaban Kasa sannan babban Kwamandan rundinar RSF Janar Dagalo tattaunawa na musamman, yace masa muna so rundinar RSF ta dawo cikin rundinar sojin Kasar Sudan a zama daya, to shi kuma Dagalo sai yaki amincewa, yace a wani dalili? shine sukace masa ai ba zai yiwu ayi rundinar soji biyu ba, kuma ba zai yiwu ayi shugaban Kasa biyu ba, haka dai suka watse ba tare da fahimtar juna ba

Shi kuma Dagalo da ya fahimci Sojin Sudan zasu bashi matsala, daga kammala wannan tattaunawa sai ya fita ya yaje da mayakansa na RSF ya fara karban iko da wasu gurare a Sudan, shi kuma shugaban Kasa Janar al-Burhan kawai sai ya fito ya ayyana RSF a matsayin rundinar 'yan ta'adda, kunga ya halatta zubar da jininsu kenan, to wannan ne babban abinda ya haddasa yakin Sudan a halin yanzu, a cikin sati guda sau uku rundinar RSF na yunkurin yiwa sojojin Sudan juyin mulki wanda ya kai ga gwabza kazamin fada

RSF Sunyi kokarin kwace babban filin tashi da saukar jiragen sama na Sudan dake Khartoum to amma Allah bai basu nasara ba, shi kuma al-Burhan sai yayi sauri ya rufe filin jirgin saboda ya san karfin abokin nasa Dagalo, saboda idan RSF suka kwace filin jirgi, wato aka bari jirage suna sauka, to abinda zai faru shine, Dagalo zai samu tallafi daga abokan huldarsa na duniya irinsu Yariman Saudiyyah Muhammad bin Salman, shugaban Kasar Egypt Janar Abdulfatah al-Sisi, shugaban Kasar Faransa Emmanuel Macron, shugaban Kasar Russia Vladimir Putin  da sauransu, musamman saboda ya yiwa Russia alkawari zai bata damar kafa sansanin soji a Sudan, ita kuma Amerika bata so, tana tare da al-Burhan

A rubutuna gaba zanyi bayani akan kudaden da ake kashewa a wannan yaki na Sudan, da salon yakin da karfin makamai da barnan da akeyi a Sudan, da kuma inda yakin ya nufa har zuwa lokacin da masana ilmin tsaro suke hasashen za'a iya kawo karshen yakin

Muna rokon Allah Ya kare bayinsa a Sudan, Ya sa yakin ya cinye wadanda suka yiwa shugaba Al-bashir zanga-zanga da tawaye


Abun Da Ya Haddasa Yakin Sudan Jamhuriyar Musulunci (Kashi na daya) - Datti Assalafiy

Datti Assalafiy✍️

Shimfida:
Akwai taba addini a yakin Sudan, saboda shi tsohon shugaban Kasar Sudan Umar Albashir wanda aka masa tawaye aka hambarar dashi da karfin tsiya ya bawa Musulunci kariya sosai a Sudan, yana bawa Musulunci kariya a Sudan wanda ko Saudiyyah bata yin irinsa a Kasarta

Yana daya daga cikin shugabannin Kasashen Musulunci a duniya wanda idan makiya Musulunci suka taba addinin Allah da Musulmai yake fitowa yayi magana, Kasar Iran daular masu bin addinin shi'ah sun taba yin mummunan batanci ga Sahabban Annabi (SAW) guda biyu Abubakar da Umar, a ranar ya kori Ambasadar Kasar Iran, kuma yasa aka rushe embassy na Iran dake Sudan, aka gina Sabon Masallaci a gurin, aka sanya wa Masallacin sunan Abubakar da Umar wato sunan Sahabban Annabi (SAW)

Lokacin Shugaba Umar Albashir babu gidan sayar da giya a Sudan, babu gidan karuwai a Sudan, babu gidan caca da sauran guraren sabon Allah, mata basa shiga harkokin shugabanci, to wannan kariyar da ya bawa Musulunci, sai Kasar Amerika ta dauki hayar wasu gurbatattun Musulmai suka tayar da zanga-zanga mai taken "HURRIYA-SALAMA-ADALA". ma'ana 'yanci, adalci da zaman lafiya, wato su sun gaji da dokokin Musulunci tsaurara suna neman 'yanci don suyi rayuwa irin na yahudu da nasara, akan haka suka kifar dashi, to Allah suka taba

A lokacin da suke dab da zasu kifar da Albashir, ya fito yayi rantsuwa yace Billahillazi zaku ce na fada muku idan kuka sake kuka hada kai da Amerika, Wallahi sai kunyi da na sanin abinda kuke min na zanga-zanga da tawaye, to bayan sun kifar dashi, shugaban Sojojin Sudan General Abdel Fattah al-Burhan da ya maye gurbinsa karen farautar Amerika da Isra'ila ne, nan take ya bude wa Kasar Isra'ila hanyar mubayi'ah, kuma kafin fara wannan yakin, a ranar 1-2-2023 General Al-Burhan ya gayyato Ministan harkokin waje na Kasar Isra'ila Eli Cohen zuwa Khartoum babban birnin Sudan, wannan ne abinda ya faranta ran Amerika ta cire manyan takunkumi da ta kakabawa Sudan lokacin mulkin Umar Albashir, kuma ta nemi Shugaban Sojojin ya mika mata Albashir don ta wulakantashi

An yaudari Mutanen Sudan da neman 'yanci, to ga inda 'yancin ya kaisu a yau, mutum sama da dubu dari uku suna sansanin 'yan gudun hijra a sati uku da aka fara wannan yakin, 'yan Sudan sama da dubu dari da hamsin sun tsere daga Kasar, an kashe mutane kusan dubu daya zuwa yanzu, asibitoci sun rufe, manyan kasuwanni sun rufe, babu inda za'a kai marassa lafiya, kafar internet na Kasar na neman rufewa gaba daya, harkokin bankuna na Kasar duk sun tsaya saboda mummunan harin bomb da akayi a babban bankin Kasar Sudan, farashin kudin Sudan yayi mummunan karyewa mafi muni a tarihi, a tsakanin sati uku da fara wannan yakin anyi barna a Sudan wanda za'a dauki tsawon lokaci kafin a gyara lamura, na karanta bayanin wani masanin tsaro yace za'a kai nan da shekaru 15 kafin Sudan ta dawo hayyacinta ko a gama wannan yakin

Wannan bayanin da nayi shinfidane kawai, ku biyoni a rubutu na gaba don jin abinda ya haddasa wannan yaki da tarihin yakin, da inda aka nufa, akwai babban darasi garemu akan wannan kazamin yaki da yake faruwa a Sudan
 
Muna rokon Allah Ya tausaya wa bayinSa salihai da kananan yara da mata dake Sudan Ya kawo musu mafita na alheri

Allah Ya sa fitinar ta cinye wadanda suka tayar da ita da wadanda suka tsara zanga-zangar kifar da shugaba Umar Albashir 


Thursday, 27 April 2023

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta


Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta.

Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan.

Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta.

Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar.

Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gida.

“Dala miliyan 1.2 (Naira miliyan 552) aka caje mu kan bas 40 da muka nema; Mun samu bas guda 40 na alfarma da za su dauki ’yan Najeriya (daga Khartoum) zuwa iyakar kasar Masar.

“Sanin kowa ne cewa tabbas irin wannan yanayi akwai wadanda za su yi amfnai da rikicin Sudan wajen tatsar jama’a,” in ji Oyema.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an gama kwashe ’yan Najeriya cikin sa’a 72 da gwamnatin Sudan ta bayar na tsagaita wuta.

“Ba mu da matsala da wa’adain awa 72 da gwamnatin ta bayar kuma mun tattauna da bangarorin da abin ya shafa, kuma sun ba mu hadin kai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa “Za a kwashe ’yan Najeriya ne a rukuni-rukuni domin tabbatar da tsaron lafiyarsu; kuma Alhamdulillah babu dan Najeriya ko daya da ya rasa ransa.

AMINIYA

Monday, 24 April 2023

Air Peace Zai Kwaso Daliban Najeriya Da Suka Makale A Sudan Kyauta

 

Kamfanin jiragen sama na Air Peace ya ce zai kwaso daliban Najeriya da suka makale a kasar Sudan inda yaki ya barke, kyauta zuwa gida.


Rikicin shugabanci ya kazance a Sudan a baya-bayan nan, har ta kai ga rufe sararin samaniyar kasar.



Akalla daliban Najeriya 5,000 da ke Sudan sun nuna matukar bukatar a dawo da su gida, inda wasu daga cikinsu ke kokarin tsallaka iyaka zuwa kasar Habasha, mai makwabtaka da Sudan.


Shugaban kamfanin Ake Peace, llen Onyema, ya sanar da cewa idan ’yan Najeriya da ke Sudan za su iya tsallaka iyaka zuwa kasashen makwabtakan Sudan, to kamfaninsa zai kwaso su zuwa gida a kyauta.



Ya ce aikin kwaso su ya wuce a bar wa gwamnati ita kadai, saboda bai kamata a yi asarar dan Najeriya ko daya ba a rikicin na Sudan.


Gwamnatin Tarayya dai ta yi alkawarin ranar Talata za ta fara kwaso ’yan Najeriyan ta kasar Habasha.


Wata sanarwa da Fadar Shugaban Kasa ta fitar ta ce Ma’aikatarta Harkokin Kasashen Waje na aiki da gwamantin kasar Habasha, domin amfani da sararin samaniyarta wajen kwashe ’yan Najeriya da suka makale a Sudan.



A ranar Asabar kungiyar daliban Najeriya da ke Sudan ta bukace su da taru a wasu wurare uku da ayyana domin kwashe su zuwa Habasha.



Tun da farko, wasu daga cikin daliban sun bayyana cewa an fara katse layin sadarwa a Sudan sakamakon rikicin, wanda suka nuna damuwa cewa hakan na iya kawo tasgaro ga yadda za a tuntube su domin kwashe su daga kasar.


AMINIYA


Saturday, 15 April 2023

Sojojinmu ne ke iko da muhimman wurare - shugaban Sudan

 


Janar Abdel Fattah al-Burhan, jagoran Sudan kuma babban hafsan hafsoshin sojin ƙasar ya musanta iƙirarin rundunar jami'ai masu kayan sarki ta RSF, cewa dakarunta ne ke iko da fadar shugaban ƙasa da hedkwatar sojoji da kuma filin jirgin sama.

A wani saƙon waya da aka naɗa lokacin hira da gidan talbijin na Al Jazeera, Janar al-Burhan ya dage kan cewa dakarunsa ne har yanzu ke da iko.

Ana ci gaba da samun rahotanni masu cin karo da juna game da abin da ke faruwa a tsawon wannan rana kan taƙamaimai wane ne ke iko da muhimman wurare a birnin Khartoum.

BBC

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...