Posts

Showing posts with the label Kyautar Kudi

Hajj 2023: Gwamna Yusuf ya ba da gudummawar naira miliyan sittin da biyar ga maniyyatan 6,166

Image
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayar da gudummawar Naira miliyan 65 ga maniyyata Jihar Kano 6,166, wadanda suka yi aikin Hajjin shekarar 2023 a kasa mai tsarki a matsayin ‘Kyautar Sallah’. A cikin sanarwar da babban sakataren Yada labaran gwaman, Sunusi Bature Dawakin Tofa, tace da Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabiu Danbappa ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wajen taron bayan Arafat da ya yi da jami’an alhazai a Makka. Ya ce kowane mahajjaci za a ba shi Riyal Hamsin Daraktan ya ce an yi hakan ne domin nuna yabawa da kyawawan halayen da mahajjatan suka nuna a kasa mai tsarki. Ya bukaci alhazan da su kashe kyautar gwamna da na guzirimsu ta hanyar da ta dace  su kuma guji kashe kudaden da za su iya hana su komawa kasar bayan sun kammala ankinsu na ibada  Daga nan ya bukaci alhazan da su ci gaba da kokarin nuna kyakykyawan kimar jiha da kasa a kasa mai tsarki. Ya ce, “Alhazan za su dawo daki-daki kamar yadda suka zo