Search This Blog

Showing posts with label Atiku. Show all posts
Showing posts with label Atiku. Show all posts

Wednesday, 1 February 2023

Atiku Abubakar Zai Kaddamar Da Makarantar Haddar Alkur'ani A Kano


 Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, zai kaddamar da makarantar sakandaren kwana ta haddar Al-Kur’ani mai dalibai 500 a Jihar Kano.

Atiku zai bude wannan makarantar haddar Al-Kur’ani ce a unguwar Gunduwawa da ke Karamar Hukumar Gezawa, a yayin ziyarar yakin neman zabensa a Jihar Kano, wadda za a gudanar ranar 9 ga watan Fabrairun da muke ciki.

Wannan makarantar haddar Al-Kur’ani “Na da wurin kwanan dalibai mata 250, maza 250, kuma za su rika haddace Al-Kur’ani a cikin wata bakwai, kafin su tafi makarnatun gaba da sakandare,” inji kakakin kwamitin yakin neman zaben Atiku a Jihar Kano, Sule Ya’u Sule.

Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau ne dai ya gina makarantar ta haddar Al-Kur’ani mai daukar dalibai 500 a matsayin aikinsa na raya alu’m

Sule Ya’u Sule ya sanara ranar Laraba cewa, Atiku zai kaddamar da makarantar ce a ranar taron yakin neman zabensa, ko kuma washegari.

A cewarsa, “Wazirin Adamawa zai zo Kano ranar 9 ga Fabrairu, don haka jama’ar Kano ku shirya ganin dan takara mai karsashi da koshin lafiya.

“Atiku ba ba irin ’yan takarar na ba newadanda cikinsu wani da kyar yake magana,  wani ko makirfon ba ya iya rikewa, wani kuma cewa ya yi ya zo Kano ne don ya yi rawa.”

(AMINIYA)

Tuesday, 31 January 2023

Muna Kan Tataunawa Da Kwankwaso Da Obi - Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Monday, 23 January 2023

Bayan Ficewa Daga Tafiyar Tinubu, Naja’atu Ta Koma Wajen Atiku

 


Fitacciyar ’yar siyasar nan ta Jihar Kano kuma daya daga cikin tsofaffin Daraktocin kamfen din dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, Naja’atu Muhammad, ta koma wajen dan takarar PDP, Atiku Abubakar.

Matakin nata na zuwa ne ’yan sa’o’i bayan ta sanar da ajiye mukamin na Tinubu, tare da ayyana ficewarta daga jam’iyyar mai mulki.

Ta tabbatar da hakan ne yayin ziyarar da ta kai wa Atiku a gidansa ranar Lahadi.

Daga bisani dai ta shaida wa Aminiya cewa yanzu tana goyon bayan takarar ta Atiku a zabe mai zuwa.

A baya dai, Naja’atu, wacce ita ce Daraktar Kungiyoyin Fararen Hula a Kwamitin Yakin Neman Zaben Tinubu, ta ce za ta gana da ’yan takarar jam’iyyun siyasa kafin ta dauki matsaya kan wanda za ta mara wa baya.

Ta ce ta dawo daga rakiyar Tinubu ne saboda a cewarta, sam ba ya iya yin tunani da kansa.

Ta ce, “Gaskiya ne yanzu ba na yin Tinubu, dalili ke nan ma da na bar jam’iyyar. Abubuwa da dama sun faru, da kyar yake iya tunani da kwakwalwarsa. Wannan ko shakka babu, mai musu kuma ya je ya nemi bidiyonsa ya kalla.

“Ni ba na la’akari da bambancin addini ko kabilanci a siyasa, shi ya sa tunanina ya fadada. Lokaci ya yi da ya kamata mu ajiye son zuciya mu ciyar da kasarmu gaba. Ba zai yiwu mu ci gaba da tafiya a haka ba. Dalilina ke nan, amma ba ni da wata nifaka a kan kowa,” in ji ta.

Sunday, 22 January 2023

Zan Kammala Aikin Tashar Jiragen Ruwa Ta Baro Idan Kuka Zabe Ni – Atiku

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya yi alkawarin kammala aikin tashar jiragen ruwa ta Baro da ke Jihar Neja, muddin aka zabe shi a zabe mai zuwa.

Atiku ya kuma ce jam’iyyarsa ce kawai take da siddabarun da za ta magance kalubalen tsaro da ya addabi kasar, musamman ma Jihar Neja.

Burkina Faso ta ba sojojin Faransa wata daya su fice daga kasarta
Ya yi wadannan alkawuran ne lokacin da yake jawabi ga wasu kusoshi da magoya bayan jam’iyyar a Minna, babban birnin Jihar Neja ranar Asabar.

Atiku ya ce PDP ce ta faro aikin na Baro rimi-rimi lokacin da take mulki, amma APC na zuwa ta yi watsi da shi.


A cewar tsohon Mataimakin Shugaban Kasar, “Muna addu’ar Allah Ya kawo zaman lafiya a Jihar nan. Kun san PDP ce kawai za ta iya dawo da zaman lafiya a Neja. Lokacin da take mulki daga 1999 zuwa 2015, akwai matsalar tsaro a Neja? Muna so mu tabbatar muku cewa muddin PDP ta dawo, matsalar za ta zama tarihi.

“Muna kuma so mu tabbatar muku cewa aikin tashar Baro da PDP ta fara, amma aka yi wasti da shi lokacin da kuka bukaci canji, yanzu kun ga canjin ko? Me suka canza? Matsalar tsaro, tsadar rayuwa ko matsin tattalin arziki?

“Muna rokonku ku dawo PDP saboda ingantuwar al’amuran tsaro da ci gana Jihar Neja da ma na Najeriya baki daya,” in ji Atiku.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban PDP na kasa, Iyorchia Ayu, wanda ya karbi tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Ahmad Musa Ibeto da dubban magoya bayansa, ya ce Allah Ya albarkaci Jihar da dimbin ma’adinai.

Amma abin takaici, duk da wadanna tarin ni’imomin, APC ta mayar da ita hedkwatar talauci da rashin zaman lafiya. Akwai lokuta da ma wasu sassan wannan Jihar suka koma karkashin ’yan bindiga. Idan kuka zabe mu, za mu kawo ci gaba mai amfani,” in ji Ayu.

Wednesday, 18 January 2023

Duk Mai Son Mukami A Gwamnanatina Sai Ya Kawo Akwatinsa Lokacin Zabe - Atiku

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce duk dan jam’iyyar da ke neman kwagila ko mukami a gwamnatinsa, sai ya nuna sakamakon zaben mazabarsa kafin a ba shi.

Atiku ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Abekuta babban birnin Jihar Ogun, yayin taron ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Atiku ya ce halartar kowanne yakin neman zaben jam’iyyar ba shi ne tabbacin samun matsayi ko kwangila a gwamnatinsa ba, jajircewa wajen ganin an kawo akwatinan mazaba ne.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya kuma ce, “Dukkanku magoya bayan PDP ne, kuma kuna so ta dawo mulki, don haka ina rokonku ku tabbatar kun kawo akwatinan mazabunku.

Yawon zuwa yakin neman zaben kafatanin ’yan takarar jam’iyya ba shi ne zai sa ka samu aiki ko matsayi ko kwangila ba idan an ci zabe, hanyar da kadai za ku samu shi ne nuna min sakamakon zaben mazabarku.

“Kuma ina bai wa kowanne dan takarar PDP umarnin yin hakan, domin da haka ne kadai za mu ci zabe.

Atiku ya kuma yi alkawarin farfado da bangaren ilimi da tattalin arziki, domin kawo karshen yajin aikin jami’o’i a Najeriya, da kuma inganta rayuwar ma’aikata da sauran al’umma.
(AMINIYA) 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...